Masu zabar sarki a masarutar zariya sun dukufa ,don  sake zabo wasu sunayen  mutanen da za’a mikawa gwamnan jihar don zabar sarki a ciki.

Hakan na zuwa ne bayan da gwamnan jihar  kaduna Nasiru El’Rufa’I  bai zabi ko mutum guda ba cikin sunan mutane biyu da masu zabar sarkin suka mikawa gwamnatin jihar.

Mai magana da yawun gwamnan  muyiwa   Adeyeye yace  sakataren gwamnatin  jihar shi ya sanar da haka, kazalika gwamantin jihar  tabawa masu zabar sarkin sake zabo  mutanen don  nada sarki a masarautar.

A makon da ya gabata ne gwamna El’Rufa’I a shafinsa na twitter  ya sanar da cewa zai nada sabon sarki a masarautar bayan  ya gama karanta wani littafin tarihin masarautar da aka rubuta a shekarar 1960.

Leave a Reply

%d bloggers like this: