Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya umarci al ummar jihar da u tashi da Azumi a gobe Litinin.

Wannan ne karo na biyu da gwamnan ya bada umarnin bayan ganawarsa da shugabannin addinin musulunci da kirista.
Gwamnan ya buƙaci al ummar da su yi azumin ne don samun zaman lafiya da bunƙasar tattalin arziƙi.

A baya bayannan ne dai gwamnan ya buƙaci shugaban ƙasa Buhari da ya sauya fasalin tsarin tsaron ƙasar don kawo ƙarshen matsalar tsaro a Najeriya
