Wasu yan bindiga sunyin awon gaba da iyalan shugaban majalisar dokokin jihar Adamawa Aminu Iya Abbas guda biyu.

Haka kuma yan bindigar sun kashe yan bijilanti biyu a wani hari da suka kai gidan shugaban majalisar dokokin jihar.
Rundunar yan sandan jihar ta bakin kakakin rundunar Sulaiman Nguroje ya tabbatar da faruwar lamarin ,yayin da yace tuni kwamishinan yan sandan jihar ya bayar da umarnin bincike akan lamarin don kubutar da iyalan shugaban majalisar da akayi awon gaba da su

