Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ASUU ta ce babu ranar komawa bakin aiki. har sai an sakar musu kuɗaɗensu.

Ƙungiyar ta ce ba zata koma bakin aiki ba sai an biyasu albashinsu.

A halin yanzu ƙungiyar na tattaunawa da mambobinta kan sabon tayin da gwamnatin tarayya ta yi musu a watan da ya gabata.

Tun watanni takwas da suka gabata ƙungiyar ta fara yajin aikin a bisa ƙin biya musu buƙata da gwamnatin tarayya ta ƙi yi.

Cikin buƙatun akwai biyan albashin da aka riƙe musu da alawu, sai dai an cimma wasu daga ciki.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: