Connect with us

Labarai

Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kano – Ba Za Mu Yi Amfani Da Card Reader Ba – Farfesa Sheka

Published

on

Hukumar zaɓe mai zaman kanta a jihar Kano KANSIEC ta ce ba za ta yi amfani da naurar tantancewa ta card reader a zaɓen ƙananan hukumomi da ke gabatowa ba.

Shugaban hukumar Farfesa Garba Ibrahim Sheka ne ya bayyana hakan a yayin taron ƙarawa juna sani wanda aka shirya dangane da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli a jihar Knao.

Ya ce ba za su iya siyan na’urar ba saboda tana da tsada kuma ba su da kudin da za su mallake ta.

Farfesa Sheka ya ce za a fara zaɓen ne daga ƙarfe takwas na safe zuwa ƙarfe uku na yamma kuma baturen zaɓe za su kammala kai sakamako zuwa ƙarfe shida.

Ya ƙara da cewa an tanadi jami’an tsaro waɗanda za sub a da gudunawa wajen tabbatar da tsaro a yayin zaɓen.

Sannan dukkan kayan zaɓe sun kammala za su fara raba su a ranar juma’a mai zuwa.

Jam’iyyu 18 ne za su shiga zaɓen da za a yi a ranar Asabar 16 ga watan Janairun da muke ciki.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Yan Bindiga Sun Sace Masu Sarautar Gargajiya A Kaduna

Published

on

Yan bindiga sun sake kai mummunan hari a karamar hukumar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna.

 

Maharan sun hallaka mutane da dama a Kakangi da Unguwar Matinja a ranar Alhamis 2 ga watan Mayu.

 

Wannan hari na zuwa ne mako daya bayan miyagu sun hallaka wasu mutane uku a Kakangi da ke jihar.

 

Yayin harin, maharan sun hallaka yan banga guda takwas tare da sace masu sarautar gargajiya na Kakangi da Kisaya.

 

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansir Hasssan ya tabbatar da haka ga gidan talabijin na Channels.

 

Mansir ya ce jami’ansu suna ci gaba da tattara bayanai domin sanin yawan wadanda suka mutu.

 

Wani shugaban a yankin, Muhammad Amin ya ce maharan sun farmaki ‘yan bangan ne lokacin da suke neman ceto wasu da aka yi garkuwa da su.

 

Amin ya ce an yi garkuwa da mutanen ne yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa jana’iza a Kakangi da Sabon Layi.

 

 

Continue Reading

Labarai

Wike Zai Yi Hadaka Da Kashashen Ketare Wajen Inganta Tsaro A Abuja

Published

on

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana aniyarsa ta yin hadaka da kasar Hungary a fannin tsaro da noma.

 

A cewar ministan, yunkurin da suka yi yana daga cikin bada muhimmanci da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wurin samar da cikakken tsaro a Abuja.

 

Mista Wike ya bayyana kudurin ne yayin wata ziyara da ya kai ofishin jakadancin kasar Hungary dake Abuja.

 

A lokacin ziyarar, ministan ya bayyana abubuwan da gwamnatin ke buƙata daga kasar Hungary domin dakile barazanar tsaro a Abuja.

 

Ya lissafa bukatar samun jirage marasa matuka da za su rika samar da cikakken tsaro a birnin tarayyar.

 

Amma sai dai ya ce akwai bukatar a tantance irin jiragen da za su dace da birnin domin kaucewa ɓacin rana da kuma kasancewarsu ingantattu.

 

Mista Wike ya kara da cewa lalle akwai matsalar tsaro a Abuja amma da yardar Allah za su magance ta idan suka samu hadakar.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Kashim Shettima Ya Roki Yan Najeriya Su Kara Hakuri Da Halin Kunci Da Suke Ciki

Published

on

Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya roki yan Najeriya da su kara hakuri a kan wahalar rayuwa da ake ciki.

 

Mataimakin shugaban kasar ya ce dukkan tsare-tsaren da gwamnatin tarayya ta fito da su musamman janye tallafin man fetur, an kawo su ne domin farfaɗo da tattalin arzikin kasar.

 

Kashim ya ce lalle nan kusa kadan da zarar an magance matsalolin da ake fama dasu ‘yan Najeriya za su sha dara.

 

Ya kara da cewa nan kusa za a ga canji nagari cikin rayuwar al’ummar kasar ta hanyar rage talauci, wadatar abinci da haɓakar tattalin arziki.

 

Mataimakin shugaban kasan ya yi jawabin ne a jiya Alhamis, 2 ga watan Mayu a wani taro da aka shirya a dakin taro na Ladi Kwali da ke Abuja.

 

 

 

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana aniyarsa ta yin hadaka da kasar Hungary a fannin tsaro da noma.

 

A cewar ministan, yunkurin da suka yi yana daga cikin bada muhimmanci da gwamnatin Bola Tinubu ta yi wurin samar da cikakken tsaro a Abuja.

 

Mista Wike ya bayyana kudurin ne yayin wata ziyara da ya kai ofishin jakadancin kasar Hungary dake Abuja.

 

A lokacin ziyarar, ministan ya bayyana abubuwan da gwamnatin ke buƙata daga kasar Hungary domin dakile barazanar tsaro a Abuja.

 

Ya lissafa bukatar samun jirage marasa matuka da za su rika samar da cikakken tsaro a birnin tarayyar.

 

Amma sai dai ya ce akwai bukatar a tantance irin jiragen da za su dace da birnin domin kaucewa ɓacin rana da kuma kasancewarsu ingantattu.

 

Mista Wike ya kara da cewa lalle akwai matsalar tsaro a Abuja amma da yardar Allah za su magance ta idan suka samu hadakar.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: