Connect with us

Labarai

An Kashe Mutane Takwas A Kaduna

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce wasu ƴan bindiga sun kai hari garin har su ka kashe mutane takwas.

An kai harin ne a Kajuru na ƙaramar hukumar Kachia a jihar Kaduna.

Kwamishinan tsaro a jihar Samuel Aruwan ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a yau.

Ƴan bindigan sun fara buɗe wuta a kan wata motar ƙirar bas da wata akori kura wanda yay i sanadiyyar mutuwar mutane biyar nan takje sai wasu da su ka jikkata.

Haka kuma ƴan bindigan sun kuma tare babbar hanyar fita daga ƙauyen Doka kuma su ka buɗe wa wata babbar mota wuta lamarin da ya  yi sanadiyyar mutuwar direban.

Sai ƙauyen Inlowo da ƴan bindiga su ka kashe mutum guda tare da sace shanu 180.

Haka kuma ƴan bindigan sun buɗe wuta a kan wata ƙaramar mota wanda yay i sanadiyyar mutuwar mutum guda da jikkata wasu a ciki.

Sanarwar ta fita ne kwana guda da bayyana cewar gwamnatin jihar Kaduna ta ceto ɗalibai biyar daga cikin waɗanda aka sace a wata kwaleji a kwanakin baya.An Kashe Mutane Takwas A Kaduna

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

NDLEA Ta Lalata Haramtattun kwayoyin A Legas Da Osun

Published

on

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) ta yi nasarar lalata haramtattun kwayoyi a jihohin Legas da Ogun.

Hukumar ta samu nasarar ne a ranar Talata, 16 ga watan Afrilu.

A cikin sanarwar da hukumar ta fitar a shafinta na Facebook, ta tabbatar da lalata jimillar kilogiram 304,436 da kuma lita 40,042 na haramtattun kwayoyi da ta kama daga sassan jihohin Legas da Ogun.

Hukumar ta lalata haramtattun kwayoyin ne da ta kama a bainar jama’a a Badagry da ke jihar Legas.

Shugaban hukumar ta kasa, Mohamed Buba Marwa ya ce lalata haramtattun kwayoyi da aka kama ya biyo bayan umarnin kotu ne.

Buba Marwa ya yi kira domin samun karin goyon bayan jama’a kan kokarin da hukumar NDLEA da sauran masu ruwa da tsaki ke ci gaba da yi na dakile matsalar shan da safarar miyagun kwayoyi a Najeriya.

Marwa ya kara da cewa kwayoyin da suka kama nau’o’i ne daban-daban da suka hada da koken, kanabis da tramol.

Shugaban ya kuma mika godiyarsa ga sarakunan gargajiya, shugabannin tsaro, malamai, kungiyoyi da sauran wadanda suka shaida lalata kwayoyin.

Continue Reading

Labarai

Babbar Kotun Tarayya Ta Jingine Dakatarwar Da Aka Yiwa Ganduje

Published

on

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya samu nasara a gaban babbar kotun tarayya da ke Kano.

 

Babbar kotun ta jingine dakatarwar da shugabannin APC na mazaɓar Ganduje, suka yi wa tsohon gwamnan na Kano.

 

Alƙalin kotun, mai shari’a Abdullahi Liman ya umurci shugabannin APC na mazaɓar Ganduje, kada su yi aiki da umurnin babbar kotun jihar na dakatar da Abdullahi Umar Ganduje.

 

Mai shari’a Abdullahi ya kuma ya hana duk waɗanda umurnin babbar kotun jihar ya shafa bin umurnin, har sai an saurari ƙarar da Ganduje ya shigar ta neman a yi masa adalci a saurari ɓangarensa.

 

Wannan umurnin dai na zuwa ne kwana ɗaya bayan babbar kotun jihar ta amince da buƙatar shugabannin APC na mazaɓar Ganduje ta dakatar da tsohon gwamnan na Kano.

 

Shugabannin dai sun dakatar da Ganduje ne saboda zargin cin hanci da rashawa da almundahana da gwamnatin jihar Kano ke yi masa.

 

Kotun ta kuma sanya ranar 30 watan Afrilu domin sauraren buƙatar da Abdullahi Umar Ganduje wacce lauyansa Jazuli Mustapha ya gabatar a gabanta.

 

Waɗanda ake ƙara a cikin ƙarar sun haɗa da Haladu Gwanjo, Nalami Mai AC, Muhammadu Baiti, Danmalam Gata, Musa Lado, Laminu Sani Barguna, Umar Sanda, Auwalu Galadima da Abubakar Daudu. Sauran sun haɗa da rundunar ƴan sandan Najeriya, kwamishinan ƴan sandan Kano, hukumar ƴan sandan farin kaya (DSS), da hukumar kare farar hula (NSCDC)

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Kano Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinoni Guda Hudu

Published

on

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya rantsar da sabbin kwamishinoni guda hudu tare da bayyana ma’aikatan da za su fara aiki.

 

Manema laba sun rawaito Gwamnan ya ambata cewa Mustapha Rabi’u kwankwaso a matsayin kwamishinan ma’aikatar matasa da wasanni, sai Abduljabbar Garko a matsayin kwamishinan kasa da na jihar kano.

 

Sannan an nada Shehu Aliyu yarmedi a matsayin kwamishinan aiyuka na musamman sai Adamu Aliyu kibiya kwamishinan kasuwanci da masana’antu na jihar.

 

Gwamnan ya Kuma ja hankalinsu da su zama masu gaskiya da rikon Amana a dukkannin lamuransu na yau da kullum.

 

Ya kuma bukace su da su maida hankali wajen tayashi sauke nauyin da al’ummar jihar kano suka dora masa.

 

In za a iya tunawa majalisar dokokin jihar kano tun a watan da ya gabata ne ta kammala aikin tantance sunayen sabbin Kwamishinonin da gwamnan ya tura musu domin nada su a matsayin Kwamishinoni.

 

Har ila yau a wannan rana gwamnan ya jagoranci rantsar da sabbin masu bashi shawara da suma majalisar dokokin jihar kano ta sahalle masa ya nada su.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: