Connect with us

Labarai

Ku Yi Aiki Da Kwarewa Don Ceto Ɗaliban Tegina – Buhari Ga Jami’an Tsaro

Published

on

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya buƙaci dukkan jami’an tsaron ƙasar da su yi aiki da kwarewa wajen ceto ɗaliban da aka sace a Neja.

Muhammadu Buhari ya bayyana haka ne a ckin wata sanarwa da mai Magana da yawunsa Malam Garba Shehu ya fitar.

Sanarwar ta umarci jami’an tsaro da su yi aiki cikin gaggawa tare da kwarewa wajen ceto ɗaliban da aka sace a makaranatar islamiyya ta Tegina a jihar.

A ƙarshen makon da ya gabata ƴan bindiga su ka shiga cikin garin tare da sace ɗaliban islamiyyar tare da malamansu ana zargin ma har da matan aure a ciki.

Shugaban makaranatar ya zanta da yan bindigan da su ka sace ɗaliban har ya buƙaci da kada su taɓa lafiyar ɗaliban da malaman su.

Sannan y ace har da ƴaƴan sa biyar a cikin waɗana aka sace a makaranatr.

Zuwa yanzu dai ya ce sun samu rahoton ɗalibai 136 waɗanda iyayensu su ka tabbatar da cewar bas u ga ƴaƴan su ba.

Ana zargin dalibai da malaman islamiyyar da yan bindiga su ka sace sun haura 200, yayin da adadin ɗaliban da ke karatu su ka kai 302.

Ƴan bindigan sun firgita mutanen garin da harbin bindiga yayin da su ka shiga makarantar da nufin sace ɗaliban.

Ko da yake an saki wasu ɗalibai da aka ce ƙanana ne.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tsadar Karatu Na Iya Sa Rabin Ɗaliban Jami’a Su Gudu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta ce kashi 50% na ɗaliban da ke karatu na iya ajiyewa saboda tsadar karatu da ake ciki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodoke ne ya bayyana haka ya ce nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa ɗaliban da ke karatu a jami’o’in ƙasar kashi 50% daga ciki na iya ajiye karatun nasu.

A wata hira da aka yi da shugaban a gidan talabiji na Channels ranar Lahadi da daddare, ya gargaɗi ɓangaren ilimi na ƙasar da su farga a kan abinda ka iya faruwa.

Sai dai ya alaƙanta ƙara kuɗin da jami’o’i su ka yi da mafi ƙarancin albashin da ake biya na naira 30,000 a ƙasar.

Sannan ya ce akwai hatsari mai yawan gaske idan aka samu ƙarin matasa masu yawa da su ka bar makaranta.

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙarawa malaman jami’a albashi da kashi 30 ga masu matsayin farfesa.

Continue Reading

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: