Connect with us

Labarai

Kotu Ta Saka Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Zakzaky

Published

on

Wata babbar kotu a jihar Kaduna ta sanya ranar 28 ga watan Yuni da muk ciki a matsayin ranar da za ta yanke hukunci a kan shari’ar da ake yi wa shugaban mabiya Shi’a Ibrahjim Zakzaky da mai ɗakin sa Malama Zinat.

Gwamnatin jihar Kaduna ce ta gurfanar da Malamin a gaban kotu bayan tare da tuhumarsa da zargin kisan kai da kuma hada taro ba tare da izini ba.

Tsawon shekaru aka kwashe shugaban mazahabar shi’a Ibrahim Zakzaky da mai dakinsa Malama Zinat ke hannun hukumar tsaro da DSS duk da cewar kotu ta bayar da belin sa.

Sai dai lauyoyin Ibrahim Zakzaky sun buƙaci kotu ta yi watsi da ƙarar saboda gaza gabatar da hujja a kai.

Amma lauyoyin gwamnati sun buƙaci a ci gaba da shari’ar saboda hujjar da su ka gabatar wa da kotu.

Tun bayan kama shugaban mabiya shi’a a jihohi daban-daban ke gudanar da zanga-zanga don ganin an saki malamin nasu.

Mabiya shi’a sun yi zargin gwamnati da ƙin barin shugaban domin samun kyakkyawar kulawa daga likitocin da za su duba lafiyar sa.

Barista Huruna magashi wani lauya daga ɓangaren Ibrahim Zakzaky ya bayyana cewar daga cikin shaidun da ɓangaren masu ƙara su ka gabatarwa kotu har guda 15 babu wadda aka samu da alaƙa da zargin da ake yi wa shugaban Shi’a Ibrahim Zakzaky da mai ɗakin sa Malam Zinat.

A kan hakan ne lauyoyin ɓangaren Ibrahim Zakzaky ƙarƙashin jagorancin Barista Femi Falana su ka miƙa roƙo ga kotun don ganin ta rufe shari’ar tare da watsi da zragin da ake masa.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Kotu Ta Dakatar Da EFCC Daga Kama Tsohon Gwamnan Kogi Yahya Bello

Published

on

Babbar kotun jihar Kogi da ke zamanta a Lokoja ta dakatar da hukumar hana cin hanci da rashawa EFCC kamawa, tsarewa tare da gurfanar da tsohon gwamnan jihar Yahaya Bello.

 

Umarnin kotun wanda ta yanke a yau Laraba, ta hana hukumar kama tsohon gwamnan har said a izinin kotu.

 

Alƙalin kotun Justice I.A Jamil ne ya karanto hukuncin byan da hukumar ta matsa don ganin ta kama tsohon gwamnan.

 

Ana zargin tsohon gwamnan da yin sama da faɗi da wasu kuɗaɗen jihar a lokacin da ya na gwamna.

 

Kotun ta soke umarnin wata kotu a jihar da ta bai wa hukumar dammar kama tsohon gwamnan.

 

A yau Laraba ne hukumar ta kai sumame don kama tsohon gwamnan a gidansa da ke Abua, sai dai daga bisani ya tsallake kamun wanda aka tseratar da shi.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

An Maida Masu Bukata Ta Musamman Baya A Cikin Gwamnatin Tarayya

Published

on

Ƙungiyar masu buƙata ta musamman ta arewacin Najeriya ta koka a kan yadda ake sake mayar da su baya duk da cewar an zaɓo ɗan cikinsu tare da bashi muƙami a fadar shugaban ƙasa.

 

Yarima Sulaiman Ibrahim shugaban ƙungiyar na arewa, shi ne ya bayyana haka yayin ganawa da Matashiya TV yau Laraba.

 

Abba Isah shi ne mashawacin shugaban ƙasa a kan masu buƙata ta musamman wanda aka zaɓo daga jihar Yobe.

 

Ya ce dun da an zaɓo ɗan cikinsu kuma aka masa mashawarcin shugaban ƙsa kan masu buƙata ta musamman, bay a yin abinda ya kamata.

 

Y ace maimakon ya mayar da hankali wajen samar da ayyukan yi ga masu buƙata ta musamman, sai ya fi karkata wajen raba abinda bai kai ya kawo ba.

 

A sakamakon haka y ace ba za su lamunta ba domin a wannan lokaci ana samun ƙaruwar mabarata daga cikinsu maimakon raguwarsu.

 

A don haka su ka yi koka domin a cewarsu, ba ya yin abinda ya kamata wajen sauke nauyin da ke wuyansa.

 

Za ku samu cikakkiyar tattaunawar a shafukanmu na YouTube da Facebook.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Rundunar Sojojin Najeriya Ta Tarwatsa Sansanin Yan Boko Haram Da ISWAP

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar gano wani sansanin mayaƙa Boko Haram da ISWAP a dajin sambisa tare da lalatashi sannan su ka ƙwato makamai.

 

A wata sanarwa da rundunar ta sanar a shafinta na X wanda aka fi sani da Twitter a baya, rundunar ta ce sun tarwatsa sansanin mayaƙan sannan sun lalata wasu makamai tare da ƙato wasu.

 

An kai harin ne Ngumne, Kawaran, Mangu duka a dazukan Sambisa da Tinbuktu a jihar Borno.

 

Rundunar ta yi amfani da makamai masu hatsari wajen tarwatsa sansanin sannan an ƙato manyan bindigu da hasashi da wasu makamai.

 

Ta ce hakan na daga cikin ayyukan da ta ke yin a kawar da dukkanin ayyukan ta’addanci da ake aikatawa a jihar.

 

Jihar Borno na fama da rikicin mayaƙan ISWAP da Boko Haram fiye da shekaru 10 da su ka gabata.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: