Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Dawo Da Karɓar Harajin Motoci Masu Zirga-Zirga A Titunanta

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya za ta dawoda karɓar harajin motoci da ke zirga-zirga a manyan titunan ƙasar.

Ministan ayyuka da gidaje a Najeriya Babatunde Fshola ne ya sanar da haka a yau Laraba bayan majalisar zartarwa a ƙasar ta amince da dawo da harajin.

Ministan ya ce an ɗauki matakin dawo da karɓar harajin ne domin faɗaɗa hanyoyin samar da kuɗin shiga a ƙasar.

Minsitan ya ce tun tuni akwai tsarin biyan harajin wanda a halin yanzu za a dawo da shi.

Tsarin harajin wwanda ake biya sama da shekaru 15 sai dai an dakatar da karɓar sa amma a wanna lokaci za a dawo da shi.

Tsarin harajin zai bai wa ƙananan motoci damar biyan naira 200 sai kuma manyan motoci da za su dinga biyan naira 500.

Karɓar harajin ba zai shafi motocin jami’an tsaro ko babura da kekuna ba, haka kuma bai shafi motocin gwamnati da ma’aikatu ba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tsadar Karatu Na Iya Sa Rabin Ɗaliban Jami’a Su Gudu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta ce kashi 50% na ɗaliban da ke karatu na iya ajiyewa saboda tsadar karatu da ake ciki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodoke ne ya bayyana haka ya ce nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa ɗaliban da ke karatu a jami’o’in ƙasar kashi 50% daga ciki na iya ajiye karatun nasu.

A wata hira da aka yi da shugaban a gidan talabiji na Channels ranar Lahadi da daddare, ya gargaɗi ɓangaren ilimi na ƙasar da su farga a kan abinda ka iya faruwa.

Sai dai ya alaƙanta ƙara kuɗin da jami’o’i su ka yi da mafi ƙarancin albashin da ake biya na naira 30,000 a ƙasar.

Sannan ya ce akwai hatsari mai yawan gaske idan aka samu ƙarin matasa masu yawa da su ka bar makaranta.

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙarawa malaman jami’a albashi da kashi 30 ga masu matsayin farfesa.

Continue Reading

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: