Connect with us

Labarai

Rashin Abba Boss Babban Giɓi Mai Wahalar Maye Gurbi

Published

on

Alhaji Muhamamd Aminu Adamu wanda aka fi sani da Abba Boss guda ne cikin jama’ar da ke talafe da rayuwar dubban mutane tare da ƙoƙarin ceto da yawa daga cikin don inganta rayuwar su.

Ya kasance ɗan kasuwa kuma manomi wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen hidimtawa jama’a da addinin musulunci.

Mutum ne da ya ɗauki nauyin marayu wajen ciyar da su shayar da su da ma tufatar da su har ma da harkar ilimin su.

Marasa lafiya da dama ke biyawa kuɗin magani ba tare da sun san wanene ya yi ba.

Kyautata mutane ya ke yi musamman idan ya fuskanci mutum na da jajircewa wajen neman na kansa ko karatu.

Ya samar da tsarin ciyarwa don marayu da iyayen marayu da ma marayun wanda ke amfana daga lungu da saƙo na jihar Kano.

Ya na daga cikin ɗabi’un sa kyautata wa tare da mutunta Ɗan’adam wajen ganin an samar da ci gaba ta hanyar hada kai.

Mutum ne mai kishi tare da ƙoƙarin zaburar da mutane masu kishi wanda hakan ya sa ya ke kulawa da mutane da dama musamman masu ƙaramin ƙarfi wajen ganin sun tsaya da ƙafarsu.

Abba Boss ya zamto guda ɗaya tilo da ake kwatance da alherinsa a ciki da wajen yankin sa.

Kiyaye lokaci, tabbatar da adalci da gaskiya na daga cikin abubuwan da ya ke bai wa muhimmanci.

Alhaji Aminu Adamu jajirtacce ne wajen ganin an samawa talaka ƴanci wajen gudanar da tsarin rayuwa tare da ingantata.

Ya na daga cikin mutanen da ke amfani da kuɗaɗen sa don wayar da kan jama’a ta yadda za su san yancin su.

Abba Boss na daga cikin mutanen da su ka ja hankalin gwamnati yayin da aka sanya dokar kulle ta KORONA har aka sassautata wanda miliyoyin ƴan Najeriya su ka fita daga ƙangin da su ke ciki a wancen lokaci.

Hidimarsa ba ta tsaya a nan ba sai da ci gaba da yin amo don ganin ya ja hankalin gwamnati a kan yadda ake tsadar kayan masarufi tare da jan hankalin ƴan kasuwa don ganin sun rangwantawa talakawa.

Wannan kaɗan kenan daga cikin kyawawan halayen da marigayi Alhaji Muhammadu Aminu Adamu Abba Boss ya bari kuma mutane ke ƙoƙarin koyi da shi.

Ya rasu a ranar Asabar 09 10 2021 ya bar mata biyu da ƴaƴa maza da mata daga cikin iyalan sa akwai jikoki a ciki.

An yi jana’izarsa ranar Lahadi 10/10/2021 a gidansa da ke unguwar Gama (B).

Allah ya ji ƙansa da rahama idan tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani amin.

Abubakar Murtala Ibrahim

(Abban Matashiya)

10/10/2021

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.

An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.

Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

Published

on

A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Continue Reading

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.

Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: