Rundunar ƴan sanda a jihar Akwa Ibom ta kama mutane 138 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a jihar.

An kama mutanen wadnada su ka haɗa da ƴan  fashi da makami garkuwa da mutane, fyaɗe da sauran miyagun ayyuka.

A yayin da yake jawabin lokacin da ya ke gabatar da masu laifin a gaban yan jarida, kakakin ƴan sandan jihar SP Odiko Mackdon ya ce an kama mutanen ne a cikin watanni uku kusa da ƙarshe na shekarar da mu ke ciki.

Daga cikin waɗanda aka kama akwai wata makauniya da aka kamata da ƙwarangwal ɗin kan mutane a gidanta.

Sai dai matar ta ce ba ta da masaniya a kan kawunan mutanen da aka samu a gidan nata.

Ƴan sandan sun zargi matar da haɗa hannu da masu amfani da sassan jikin mutane don wata buƙata ta daban.

Tuni rundunar ta duƙufa don zurfafa bincike a kan mutanen da aka kama sannan za su gurfanar da su a gaban kotu da zarar sun kammala bincike.

Leave a Reply

%d bloggers like this: