Connect with us

Labarai

Badaƙalar Kuɗaɗe – Malajisar Dattawa Ta Buƙaci Minsitan Ruwa Ya Bayyana A Gabanta

Published

on

Sanata Cliffford Ordia ya ce babu wani aiki da ma’aikatar damar da ruwan sha ta yi da kuɗaɗen da su ka ciyo a baya a don haka su ke so ministan reuwa Sulaiman Adamu ya zo domin yi bayani a kan badaƙalar kuɗaɗen.

Majalisar dattawan Najeriya ta yi watsi da bukatar ciyo bashi da ma’aikatar samar da ruwan sha ta buƙata har naira biliyan 287 da ɗoriya.

Ma’aikatar ta aike da buƙatar hakan ne domin gudanar da ayyukan samar da ruwan sha a birnin da karkara na ƙasar.

Majalisar ta buƙaci shugaban hukumar ya yi mata bayani dangane da bashin da aka ciyo a baya wanda aka yi da nufin samar da shirin samar da ruwan sha.

Shugaban kwamitin samar da ruwna sha a majalisar dattawa Sanata Cliffford Ordia ya buƙaci ministan ruwa ya bayyana a gaban majalisar domin yin bayan i a kan kuɗaɗen da hukumar ta ciyo bashi a baya da nufin ayyukan samar da ruwa a Najerya.

A baya hukumar samar da ruwan ta ciyo bashin dala miliyan 450, da kuma bashin dala miliyan 700 duka domin ayyukan samar d aruwa.

Shugaban kwamitin ya ce duk da amince masa na ciyo bashin a baya babu wani sakamako da ya bayyana a fili na ayyukan kudin da aka ciyo bashin.

A farkon shekarar da mu ke ciki ne Mujalar Matashiya ta zaƙulo wasu yankuna a jihar Kano da ke maƙaftaka da mahaifar ministan waɗanda ke shafe kwana da kwanaki kafin su sami ruwan da su ke sha bayan yin doguwar tafiya mai nisa.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas

Published

on

Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

 

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.

 

Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.

 

Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.

 

Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.

 

Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.

Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.

Continue Reading

Labarai

Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano

Published

on

Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.

Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: