Connect with us

Labarai

Ƴan Sanda Sun Cafke Mutane Biyar Kan Kisan Ma’aurata A Jigawa

Published

on

Rundunar yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar wasu ma’aurata mata da miji a Malammadori ta jihar.

An kashe mutanen biyu a ranar 13 ga watan da muke ciki da msialin ƙarfe 2:30 na dare.

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar ya ce wasu da ake zargin ƴan bindiga ne su ka je gidan ma’auratan da daddare sannan su ka kashe mata da miji.

Sun je gidan mutanen da ke ƙauyen Kebberi sannan su ka harbe su da bindiga.

An kashe Ahaji Musa da matasa Hajiya Adama wanda ake zargin wasu aka ɗauka da nufin kashe su har lahira.

Kakakin ƴan sandan ya ƙara da cewa ƴan bindigan ba su ɗauki komai a cikin gidan ba bayan sun kashe su.

Sai dai an sami wasu wayoyin hannu guda biyu da ake zargin na ƴan bindigan ne kuma za su gudanar da bincike a kan su.

Sannan an cafke was mutane biyar da ake zargi da hannu a kan mutuwar ma’auratan biyu wanda a halin yanzu ake kan bicike a kan su.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Gwamnatin Osun Za Ta Rage Kashi 50 Na Kudin Shinkafa Ta Saidawa Yan Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Ogun za ta fara siyarwa da ƴan jihar shinkafa tare da yin rahin kashi hamsin na kuɗin da ake siyar da ita a kasuwa.

 

Gwamnan jihar Prince Dapo Abiodun ne ya samar da haka, ya ce gwamnatinsa za ta yi hakan ne domin rage raɗaɗin matsin tattalin arziƙi da akee fama a jihar.

 

Gwamnan ya ceza a fara siyarwa da ma’aikatan gwamnatin jihar shinkafar a farashi mai rahusa, domin sauƙaƙa musu kan halin da ake ciki.

 

Gwamnan wanda ya yi bayanin yayin buɗe bakin azumi ranar Talata, ya ce dukkanin ma’aikatan gwamnatin jihar za su samu shinkafar a wannan farashi.

 

Tuni aka kafa kwamitin da zai kula da harkokin siyar da shinkafar ga ma’aikatan.

 

Sannan an gwamnatin za ta fara da siyarwa da ma’aikata ne daga bisani a kai ga sauran mutanen ƴan asalin jihar.

 

Kuma an ɗauki matakin yin rangwamen ne domin ɗorewa da cigaba da siyarwa mutanen jihar a farashi.

 

A cewar gwamnan, idan aka ce za a raba abincin kyauta lamarin ba zai ɗore ba.

 

Sai dai gwamnan ya ce za a baiwa talakawa da tsofaffi da ba za su iya siya ba shinkafar kyau

 

 

Continue Reading

Labarai

Sojoji Sun Hallaka Ƴan Bindiga Da Boko Haram A Katsina Da Borno

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar hallaka ƴan bindoga da mayaƙan Boko Haram a jihohin Borno da Katsina.

 

An hallaka mutane uku da ake zargi na daga cikin ƙungiyoyin a jihohin biyu.

 

Sannan an samu nasarar kuɓutar da dabbobi masu yawa bayan da aka hallakasu.

 

A wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Laraba, ta ce nasarar na zuwa ne bayan musayar wuta da maharan.

 

Sannan sun samu nasarar ne a jiya Talata wanda ta kai ga kwato bindigu biyu ƙirar AK47 da harsasai masu yawa.

 

A cikin jawabin sanarwar, rundunar ta ce sun kai harin ne a Garin Rinji da ke ƙaramar hukumar Batsari, da kuma yankin Gori a ƙaramar hukumar Gwoza ta jihar Borno.

 

Haka kuma akwai babur guda ɗaya da rundunar ta kwato.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Juma’a Da Litinin Matsayin Ranar Hutu Ga Ma’aikata

Published

on

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ayyana ranakun Litinin da Juma’a a matsayin ranar hutu ga ma’aikata.

 

Za a yi hutun Esta a ranakun Juma’a 29 ga watan Maris da kuma Litinin 1 ga watan Afrilu mai kamawa.

 

Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya sanar da hutun yau a madadin gwamnatin tarayya.

 

A sanarwar mai ɗauke da sa hannun Dakta Aishetu Gogi-Ndayako sakatariyar din-din-din a hukumar, sanarwar ta hori yan ƙasar da su kasance masu yafiya, nuna soyayya a ranakun hutun.

 

Sannan aka bukaci mabiya addinin kisita da su yi amfani da lokutan wajen kawo cigaba mai ma’ana a Najeriya.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: