Labarai
Awanni Kaɗan Da Tare Hanyar Kaduna Ƴan Bindiga Sun Sake Sace Wasu Mutane A Hanyar Abuja


Wasu da ake zargi masu garkuwa da mutane ne ɗauke da makamai sun sake tare babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja a yammacin jiya Litinin.

Kwana guda da sace mutane tare da kashe wasu a babbar hanyar, ƴan bindigan sun sake tare babbar hanyar tare da sace wasu mutane da dama.
Wani da abin ya faru a gabansa ya shaida cewar ya hangi motar Zamfara mai ɗaukar mutane 18 da wasu motoci hudu duka babu kowa a ciki.

Al’amarin ya faru a yammacin ranar Litinin ƙasa da awanni 24 bayan ƴan bindigan sun tare babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja a ranar Lahadi.

Motocin da aka hanga yashe a kan titi akwai alamun harbin bindiga a jikin su, kuma wajen da abin ya faru tazarar kilo mita biyar ne da wrin da aka tare ranar Lahadi.

Shaidar da abin ya faru a gabansa ya ce jami’an tsaro sun je wajen amma kafin zuwna su ƴan bindigan sun tafi da mutanen da su ka sace cikin daji cikin kanaƙanin lokaci.
Yayin da mu ka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ƴan sandan Kaduna Mohammed Jalige ya ce zai bincika a kan lamarin kuma har lokacin da mu ke kawo muku labarin ba mu ji daga gareshi ba.
Labarai
Sheikh Ahmad Gumi Yayi Allah Wadai Da Kashe Al’umma Masu Taron Maulidi A Kaduna


Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya yi Allah-wadai da hallaka mutane da jirgin soji yi a garin Tudun Biri a Jihar Kaduna.

Malamin ya bayyana hakan ne ta cikin wani jawabi da ya fitar a shafinsa na Facebook, Gumi ya ce lamarin abin takaici ne da ke yawan faruwa a yankin Arewacin Kasar.
Sheikh Ahmad Gumi ya kara da cewa ana maida Jihohin Arewacin Kasar tamkar zirin Gaza, kamar yadda sojojin Israila su ke hallaka mutanen kasar Falasdin.

A jawabin na Gumi ya zargi hukumomin Kasar da nufi mara kyau ga mutanen Kasar, tare da yin kisan kare dangi da ganganci ga al’ummar da ke kauyukan Arewa.

Gumi ya ce hakan ba zata taba yuwuwa ba jirgin yayi kuskure wajen sanya bam ga masu fararen kaya ba.

Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana cewa akwai wata a kasa wajen sanyawa masu taron mauludin bom din da jirgin yayi.
Labarai
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayarwa Da Peter Obi Martani Akan Sukar Shugaba Tinubu


Fadar shugaban kasa ta yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party ga Peter Obi raddi akan yadda ya ke sukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Martanin ya fito ne daga ofishin Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ta bakin mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha a ranar Talata.
Sanarwar ta zargi Peter Obi da bata gwamnatin Tinubu bisa rashin nasarar da ya samu a lokacin zaben kasar.

Sanarwar ta ce Peter ya yi amfani da zargin zuwa taron COP na 28 da shugaban ya tafi da mutane 1411, domin cimma wata manufa tasa ta siyasa ta hanyar yaudara.

Sanarwar ta ce Obi ya shafe tsawon lokaci ya na sukar gwamnatin ta Tinubu domin ya nuna cewa ya na kishin kasa, kuma ba gaskiya yake fada ba a kalamannasa.

Martanin na zuwa ne bayan da Peter Obi ya soki gwamnatin tarayya akan kudin da aka kashe wajen zuwa taron dumamar yanayi na COP karo na 28 da kuma shirin gyara gidan mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima.
Labarai
Kar Gwamnatin Tarayya Ta Fara Tunanin Yafe Kisan Da Sojoji Suka Yiwa Mutane A Kaduna – Sheikh Yahaya Jingir


Shugaban Majalisar Malamai na Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah ta Kasa, Sheikh Muhammad Sani Yahya Jingir, ya bayyana cewa kada gwamnatin kasar ta fara batun cewa a yafe kisan da sojoji suka yi wa mutane a gurin taron Mauludi a Jihar Kaduna, domin Allah ya yi umarnin a hukumta dukkan wanda ya aikata irin haka.

Sheikh Yahya Jingir ya bayyana hakan ne yayin wani taron ganawa da manema labarai da ya yi a gidansa da ke garin Jos.
Jingir ya ce kisan gilla da aka yiwa mutanen abu ne wanda ba za a taba lamunta ba, kuma ba za a barshi haka ba, ba tare da an hukumta wadanda suka aikata aika-aika ba.

Shugaban ya kara da cewa dole ne a hukumta dukkan wanda aka samu da hanu akan lamarin,kisan mutanen da basuji ba su gani ba,kuma hakkin kowanne shugaba ne ya kare rayukan al’ummar da ya ke jagoranta.

Jirgin ya ce hukunta wadanda suka kashe mutanen da basuji ba su gani ba shine kyakkyawan shugabanci ga kowanne irin shugaba.

Ya ce Allah Ya haramta kisan bayin Allah, ko Musulmi ne ko Kirista ne ko wanda ba shi da addini ne, domin yana da daraja da ’yancin rayuwa, a wajen Allah.
Malamin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta kafa kwararran Kwamitin bincike, wanda zai binciko musabbabin hallaka mutane.
Malamin ya yi kira da jami’an sojin da sauran hukumoomin tsaro a Kasar,da su dunga tsara yadda za su gudanar da ayyukansu kafin yi,domin kaucewa aikata ba dai-dai ba.
Daga karshe Malaman Jingir ya mika sakon ta’aziyarsa ga Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na lll da Sarkin Zazzau da gwamnan Jihar ta Kaduna da kuma ‘yan uwa da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hari.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?