Labarai
Annobar Da Za Ta Ɓulla A Nan Gaba Ta Fi Korona Saurin Kisa

Guda cikin waɗanda su ka samar da rigakafin allurar Korona ta Astra Zeneca Farfesa Dame Sarah Gilbert ta ce annoba ta gaba ta fi Korona shaɗari.

Farfesa Dame ta ce annobar da ka iya zuwa a nan gaba ta fi ta Korona saurin yaɗuwa sannan ta na da saurin kisa.
Annobar da ake tsammanin za ta iya bayyana a nan gaba na da matukar haɗari kuma ta na da saurin yaɗuwa a cikin jama’a.

Farfesa Sarah ta ce ya kamata a samar da bayanan sirri tare da zuba jari musamman ga masu bincike da kuma kamfanoni domin kare mutane a fadin duniya.

Ta bayar da misali da aikin soja wadda ta ce a kan tattara bayanan sirri tare da zuba jari don kare hare-hare domin tsare al’umma.
Haka kuma ta shawarci duniya domin ganin an ɗauki matakan kariya daga sabon nau’in Korona na Omicron bayan samun ƙarin bayanai a kan sabon nau’in cutar.
Labarai
Ma’aikatan Filayen Jirgin Sama A Najeriya Za Su Haramtawa Jirage Tashi A Najeriya

Ƙungiyoyin ma’aikatan jiragen sama na Najeriya sun yi barazanar rufe dukkan filayen sauka da tashin jiragen sama na Kasar daga ranar 31 ga watan Maris din nan da muke ciki.

Ma’aikatan sun yi barazanar rufe filayen jiragen Kasar ne, tare da nema gwamnatin tarayya da ta dauki matakin kora ga jami’in hukumar hana fasa kauri ta Kasa kwastam da ake zargi da hannu wajen cin zarafin daraktan tsaro a hukumar kula da filayen jiragen sama ta Kasa.
A wata sanarwa da gamayyar kungiyoyin suka fitar sun nuna rashin aminta da abin jami’in na Kwastom ya aikata.

Sannan kungiyoyin sun kuma nuna rashin jindadunsu bisa yadda ake samun yawaitar cin zarafin ma’aikatan hukumar kula da filayen jiragen saman Kasa.

A Bangaren hukumar ta kwastam ta ce rashin fahimtar da ya faru tsakanin jami’inta da Ma’aikatan filin sauka da tashin jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Jihar Legas ya ce rashin fahimta ne.
Mai magana da yawun hukumar na Kasa Abdullahi Mai Wada Aliyu ya ce hukumar na kokarin ganin ta hada kai tsakanin bangaren, don ci gaba da gudanar da aiki yadda ya kamata.
Labarai
INEC Ta Ki Amince Da Bukatar Yiwa Sanata Natasha Kiranye

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC Hukumar INEC ta ki amincewa da bukatar neman tsige Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, bisa rashin rubuta adireshinsu, lambobin wayarsu, ko kuma gmail din a cikin wasikar da suka aikewa da hukumar.

INEC ta ki amincewa da bukatar ne ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Talata, mai dauke da sa hannun kwamishinan hukumar Sam Olumekun.
Sanarwar ta ce bayan mika bukatar yiwa Sanata Natasha kiranye da ‘yan Mazabarta su ka yi ga hukumar, sun gudanar da zama akan batun a taron da saba gudanarwa Mako-mako.

Hukumar ta kara da cewa hanyar dakatar da dan majalisa na cikin kundin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999, da dokar zaɓe ta shekarar 2022 da ta gabata da kuma ka’idojin hukumar na shekarar 2024.

Hukumar ta ce takardun korafe-korafen da ake kai’wa hukumar daga yankin na Kogi ta Tsakiya na hade da jakunkuna shida na takardu da aka bayyana na dauke da sa hannun sama da rabin masu zabe 474,554 ne daga rumfunan zaɓe 902 a yankunan rajista 57 da ke cikin kananan hukumomin Adavi, Ajaokuta, Ogori Magongo, da kuma Okehi da Okene.
Hukumar ta bayyana cewa wakilan masu shigar da korafi ba su cika dukka wata ka’idoji da ake bukata ba wajen yiwa dan Majalisar kiranye ba.
Sanarawar ta ce Adireshin da aka sanya a cikin takardar shi ne Okene a jihar Kogi, wanda ba tare da bayyana cikakken guri ba da za a iya tuntuɓarsu, sannan sun kuma bayar da lambar waya ta babban jagoran masu ƙorafi kadai maimakon lambobin dukan wakilan masu ƙorafi.
Hukumar ta ce da zarar an cika dukkan sharruddan Korafi tare da bin ka’idojin, hukumar za ta fara guanar da tantance sa hannun a rumfunan zaɓe ta hanyar tsari na buɗe ido da zababbun masu ƙorafi kadai za su shiga.
Acewar Hukumar za ta bi dukkan doka wajen tantance dukkan korafe-ƙorafen da ake aikawa hukumar.
Labarai
Gwamnan Riko Na Rivers Ya Nada Sakataren Gwamnatin Jihar

Gwamnan riko na Jihar Rivers Ibok-Ete ya nada Farfesa Ibibia Lucky Worika a matsayin sabon Sakataren gwamnatin Jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar daga fadar gwamnatin Jihar a yau Talata.
Sanarwar ta bayyana cewa nadin Lucku ya biyo bayan yin nazari kan ƙwarewa da gogewarsa a bangarori daban-daban.

Sanarwar ta kuma ce nadin Worika ya kuma yi daidai da manufarsa ta amfani da kwararru daga jihar Rivers domin samar da tabbataccen zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar.

Nadin Sakataren na kuma zuwa ne a daidai lokacin da gwamnan rikon ya amince da yin murabus din Shugaban Ma’aikatan gwamnatin Jihar George Nwaeke.
Inda kuma gwamnan rikon ya nada Iyingi Brown wanda ya kasance babbar sakataren ofishin shugaban Ma’aikatan Jihar, inda kuma zai zauna a matsayin mai rikon mukamin shugaban Ma’aikatan har zuwa lokacin da za a nada wani sabon shugaban Ma’aikatan.
-
Labarai1 year ago
Mafi Karancin Sadaki A Najeriya Ya Koma Dubu 99,241
-
Mu shaƙata2 years ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Labaran ƙetare6 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Al'ada6 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labarai6 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini5 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Lafiya6 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Mata adon gari6 years ago
Sinadarin gyaran gashi – Adon Gari