Mai bai wa shugaban ƙasa shawara a kan al’amuran tsaro a Najeriya Babagana Munguno ya fallasa wasu ƙungiyoyin addini guda uku da ke goyon bayan ayyukan yan bindiga a Najeriya.

Babagana Munguno ya bayyana haka ne a wani taron malamai da limamai da ya gudana a Abuja.

Ƙungiyoyin su ne Jama’atr Nasr Al-islam Wal Muslimina (JNIM) da Islamic And Muslim Support Group (IMSG) sannan Islamic State in Greater Sahara (ISGS).

Ya ce daga cikin su akwai wadanda ke iza wutar rikici a kasashe Mali, Niger da Burina Faso.

Munguno ya buƙaci limamai da masu da’awa da su mayar da hankali wajen ci gaba da wa’azi a kan muhimmancin zaman lafiya tare da bai wa jami’an tsro haɗin kan da ya dace.

Leave a Reply

%d bloggers like this: