Hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayar da tabbacin kawo ƙarshen korona a cikin shekarar 2022.

Shugaban hukumar Tedros Adhanom ne ya bayyana haka ya ce zai yuwu a kawo ƙarshen cutar muddin ƙasashen duniya su ka hada kai aka yi aiki tare.

Ya ce akwai buƙatar ƙara dagewa a kan yadda duniya ke tafiyar da daƙile cutar a halin yanzu.

Hukumar ta buƙaci a yi wa kashi 70 na mutanen duniya riga-kafin cutar Korona domin sauƙaƙa dokokin da aka saka wa don hana yaɗuwarta.

Haka kuma akwai buƙatar ƙasashe su sake zage damtse domin ganin an kawo ƙarshen cutar a faɗin duniya.

Tuni wasu ƙasashen duniya su ka fara mayar da dokokin da za su taƙaita yaduwar cutar a cikin jama’a ciki har da ƙasar saudiyya.

Hukumar na kira ga al’umma da su ci gaba da bin matakan kariya domin hana yaɗuwar cutar tare da kawo ƙarshenta baki ɗaya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: