Connect with us

Labarai

Yadda Aka Ƙone Mata Da Yara Da Ransu A Zamfara

Published

on

Ƴan bindigan sun kai hare-haren ne cikin ƙauyuka 10 na jihar Zamafara sannan ake zargi sun hallaka sama da mutane 200 a ƙasa da awanni 48.

Rahotanni daga jihar Zamfara na tabbatar da cewar an gano gawarwakin mutane 143 na mutanen da ƴan bindiga su ka kashe a wasu hare-hare da su ka kai wasu ƙauyukan jihar.

An kai hare-haren ne a ranakin Laraba da Alhamis a ƙananan hukumomi Anka da Bukuyyum.

Rahotannin na cewar ko a jiya Juma’a sai da aka gano wasu gawarwaki da ƴan bindiga su ka kashe, sannan ana ci gaba da lalubo wasu gawarwakin a cikin dazukan ƙauyukan.

Wani mazaunin garin ya tabbatar da cewar an hallaka sama da mutane 200 wasu da dama an ƙone su da ransu a cikin gidajen su daga cikin mutanen da aka ƙone da ransu akwia mata da ƙananan yara.

Ya ƙara da cewa ƴan bindigan sun tilasta wa mutanen zama a cikin gida sannan su ka banka wa gidajen wuta har su ka rasa rayukansu.

Ƙauyukan Rafin Danya, Barayar Zaki, Rafin Gero, Kurfa na daga cikin ƙauyukan da lamarin ya shafa.

Haka zalika wani da lamarin ya faru a gabansa wanda ya sha da kyar ya ce yan bindigan sun kore shanu da sauran dabbobi wadanda ba su gaza 3,000 ba.

Wani mai suna Malam Muhammad Sani ya ce har yanzu ƴan bindigan su na garin kuma sun hana yin jana’zar wasu da aka gano gawarwakin su a ƙauyen su.

Rundunar ƴan sandan jihar ta ce ta na ci gaba da bincike domin tattara bayanan alƙaluman mutanen da su ka rasa rayukansu a sanadiyyar hare-haren.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

An Kone Ofishin Yan Sanda A Anambra

Published

on

Wasu ƴan daga sun kai hari tare da ƙone ofishin ƴan sanda a jihar Anambra.

 

An kai harin ne ofishin ƴan sanda na Neni da ke ƙaramar hukumar Anaocha a jihar da misalin ƙarfe 02:00am na dare wayewar yau Alhamis.

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Tochukwu Ikenga ya ce mutanen sun kai harin ne da abin fashewa da ake zargi bam ne.

 

Sannan ya ce maharan ba su ɗauki makaman jami’an ko yin garkuwa da jami’an su ba.

 

Ya ƙara da cewa, maharan sun gudu bayan da ƴan sanda su ka ci ƙarfinsu.

 

Zuwa yanzu ana ci gaba da hibiya don gano su waye su ka kai harin tare da kamasu.

 

Sai dai bai bayyana asarar da aka yi ba a sakamakon harin da aka kai.

 

 

Continue Reading

Labarai

An Kama Ƴan Fashin Da Su Ka Yi Wa Matar Aure Fyaɗe A Jigawa

Published

on

Rundunar ƴan sanda a jihar Jigawa sun kama wasu mutane uku da ake zargi da aikata fashi da makami haɗi da fyaɗe ga matar aure a jihar.

 

Kwamishinan ƴan sandan jihar AT Abdullahi ne ya bayyana haka yau Alhamis.

 

Ya ce an kama mutane uku bayan da su ka shiga gidan wani Mudan Ibrahim mazaunin ƙauyen Chori a ƙaramar hukumar Ringim tare da yi masa fashi daga bisani su ka yi wa matarsa fyaɗe.

 

Ƴan sandan sun samu labarin ne a ranar 17/03/2024.

 

Bayan zurfafa bincike, jami’an sun kama wani Umar Ibrahim, Umar Nasara, da wani Abubakar Isah dukkaninsu mazauna ƙauyen Chori a jihar.

 

Tuni aka ci gaba da zurfafa bincike a kai, kuma da zarar an kammala za su gurfanar da su a gaban kotu kamar yadda kwamishinan ya shaida.

 

A wani labarin kuma kwamishinan ya bayyana nasarar kama wasu ƴan fashi da makami, da kuma wasu da ake zargi da aikata sata a jihar.

 

 

Continue Reading

Labarai

Malamin Makaramtar Firamare Na Kuriga Ya Mutu A Hannun Ƴan Bindiga Kafin Kuɓutar Da Dalibai

Published

on

Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya sha alwashin ɗaukar nauyin karatun ɗalibai 137 da aka kuɓutar daga hannun ƴan bindiga.

 

Ɗaliban su ne waɗanda aka yi garkuwa da ssu daga makarantar firamare ta Kuriga a jihar.

 

Gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun nasu ne daga matakin Firamare zuwa sakandire ƙarƙashin cibiyar Uba Sani Foundation.

 

Gwamnan ya bayyana haka yau Alhamis kafin mayar da ɗaliban zuwa Kuriga.

 

Ya ce bayan kuɓutar da su, an ɗauki lokaci domin duba lafiyarsu kafin miƙasu ga iyayensu.

 

Ya ce guda cikin malaman da aka yi garkuwa da su mai suna Malam Abubakar, ya rasa ransa a hannun ƴan bindigan.

 

A sakamakin haka, gwamnan ya ce zai ɗauki nauyin karatun ƴaƴan malamin, tare da bai wa iyalansa naira miliyan goma.

 

Akwai waɗanda su ka samu larurar kwakwalwa daga cikin ɗaliban da aka kuɓutar, a don haka su ka miƙasu ga kwararrun likitoci domin duba lafiyarsu.

 

Sannan gwamnatin ta bayar da umarnin yin wasu ayyuka a Kuriga, wamda gwamnan ya ce garin na daga cikin garuruwan da su ka fi zaman lafiya a jihar.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: