Connect with us

Labarai

Ƴan SandaA Jigawa Sun Kama Ƴan Bindigan Da Su Ka Hallaka Jami’ansu Biyu

Published

on

Daga Amina Tahir Muhammad

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta sanar da kama wasu masu garkuwa da mutane, wadanda ake kyautata zaton suna da hannu wajen kashe jami’an ‘yan sanda biyu, da yin garkuwa da surukin wani dan kasuwa da sauran miyagun ayyuka a yankin Arewa maso yammacin jihar.

Hakan dai ya biyo bayan farmakin da aka kai wasu maboyar ‘yan ta’adda guda uku a kauyukan Dajin Maizuwo, Dan Gwanki da Yandamo dake karamar hukumar Sule Tankarkar ta jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Sale Tafida, yayin da yake gabatar da wadanda ake zargin a hedikwatar da ke Dutse a ranar Alhamis, ya ce an cimma nasarar hakan ne biyo bayan samun rahoton sirri da aka samu.

An yi holen mutane 14 da suka hada da maza goma da mata hudu, ciki har da wanda ake zargin ƴan asalin jihar Kaduna ne.

Kayayyakin da aka kwato daga hannun wadanda ake zargin sun hada da AK-47 guda uku, harsashi 308 mai girman mita 7.6, Bindigogin Mashin Janar guda daya, (GPMC), tsabar kudi naira miliyan biyu, Addina, wayar  salula shida da sauran kayayyaki.

Idan ba a manta ba Mujallar Matashiya ta kawo muku labarai a kan sace wani mutum a jihar tare da hallaka ƴan sanda biyu a ƙarsehn makon da ya gabata.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

‘Yan Takarar Gwamnoni A Jam’iyyar PRP Sun Koma SDP

Published

on

‘Yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PRP a zaben 2023 na sun sauya sheka zuwa jam’iyyar SDP.

Shugaban kungiyar ‘yan takarar gwamnan a PRP Malam Hayatuddeen Lawai Makarfi ya tabbatar da ficewarsu daga PRP zuwa SDP.

Shugaban kungiyar ya bayyana cewa sun dauki matakin koma SDP ne domin tsamo kasar nan daga halin da take ciki.

Lawai Makarfi wanda ya yi takarar gwamna a jam’iyyar ta PRP a Jihar Kaduna, ya bayyana cewa mutane na sauya sheka zuwa SDP ne bisa yadda da shugabancinta.

Makarfi ya ce sauya shekar su wani shiri ne na hadin domin kubtar da Najeriya daga shugabanci mara kyau, inda kuma ya nuna damauwarsa bisa yadda ake ci gaba da samun zubar jini, karuwar takauci, ya yin da hukumomin gwamnati ke durkushewa, inda kuma jam’iyyar APC da PDP suka mayar da mulkin kasar tamkar kasuwanci.

Kungiyar ‘yan takarar gwamnan ta kuma mika godiyarta ga PRP bisa damar da ta ba su a siyasa, inda suka ce a halin yanzu sun koma kan hanyar gaskiya.

Shugaban jam’iyyar SDP Malam Shehu Musa Gabam ya shaida musu cewa jam’iyyar za ta bai’wa masu sauya shekar dukkan wata dama da ta kamata.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya Sama 1,000

Published

on

Gwamnatin Kaduna Jihar ta amince da daukar ma’aikatan lafiya 1,800 a fadin Jihar.

Kwamishiniyar lafiya ta Jihar Hajiya Umma Ahmad ce ta tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis.

Sanarwar ta ce gwamnatin Jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Uba Sani za a dauki Ma’aikatan ne domin cike gurbin Ma’aikatan a dukkan cibiyoyi kiwon lafiya matakin farko na Jihar.

Sanarwar ta kara da cewa daukar Ma’aiktan hakan zai kara tabbatar da ci gaban Jihar akan matsayin da ta ke dashi a fannin kiwon lafiya matakin farko a Najeriya.

Kwamishinyar ta kuma ce daukar ma’aikatar zai kawo karshen karancin ma’aikata da ake samu a cibiyoyin kiwon lafiyar, tare da raguwar yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da kananan yara, da kuma kara inganta lafiyar mutanen Jihar.

Acewarta a halin yanzu ana ci gaba da gyaran cibiyoyi 255 na kiwo lafiya matakin farko, yayin da za a daga martabarsu zuwa mataki na biyu, da samar da kayan aiki na zamani, tare da bayar da muhimman magunguna duk a kokarin da gwamnatin Jihar ke yi na inganta bangaren kiwon lafiya.

Kwamishinar ta kuma ce cibiyoyin za su dunga aikin duba masu cutuka daban-daban da suka hada da ciwon suga da bai yi karfi ba, hawan jini shima da bai yi karfi ba, da bayar da tallafin wajen haihuwa da dai sauransu.

Continue Reading

Labarai

Majalisar Wakilan Za Ta Haramtawa Masu Shekaru Sama Da 60 Tsayawa Takara

Published

on

Majalisar wakilan Najeriya ta tsallake karatu na biyu kan kudurin da zai haramtawa ‘yan takarar shugaban Kasa, da na gwamnan masu shekaru sama da 60 tsayawa takara.

A zaman Majalisar na yau Alhamis, da kudurin ya tsallake karatu na biyu, bayan da dan Majalisar Hon Ikeagwuonu Ugochinyere ya dauki nauyin kudurin da ke bukatar canza wasu bangarori na kudin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999.

Rahotanni sun bayyana cewa da zarar kudurin ya tsalle karatu na uku, kuma shugaban Kasa ya sanya hannu akansa, hakan zai sauya fasalin tsayawa takara a Kasar.

Daga cikin abubuwan da kudurin ya kunsa sun hada da, dukkan wanda ya haura shekaru 60 da haihuwa b azai tsaya takarar shugaban Kasa ba, ko gwamna a Kasar.

Sannan kuma wajibi dukkan dan takara ya kasance ya mallaki shedar digirinsa na farko a bangaren da ya fi kwarewa akai, a matsayin mafi karancin takardar karatu.

Ya yin da kuma kudin ya bukaci yin gyara a sashe na 131 na kudin tsarin mukin Kasa, na bukatar iyaknce shekaru ga kowanne dan takarar shugaban Kasa, tare da sashi na 177 ga gwamomin Jihohi.

Baya ga wannan kuduri majalisar ta kuma amince da wasu kudurori daban-daban da suka shafi ci gaban Najeriya.

 

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: