Connect with us

Labarai

Kundin Tsarin Mulki Ya Bai Wa Mata Musulmi Dama Saka Hijabi – Adamu

Published

on

Minstan ilimi a Najeriya Malam Adamu Adamu ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya bayar da dama ga muaulmi su sanya hijabi a makarantu.

Ministan na wannan jawabi ne a yayin da ya halarci wani taro da mata muaulmi su ka shirya don ɗabbaƙa ranar hijabi ta duniya.

Malam Adamu Adamu wanda Hajiya Sidiƙat ta wakilce shi a wajen taron, ya ce abin takaici ne ganin yadda wasu ke sukan hakan a cikin kasar.

Ya ce kundin tsarin mulki ya bayar da dama ga yan ƙasa domin bin duk addinin da su ke so tare da bin tsarin da ke cikin sa.

Ya ƙara da cewa saka hijabi koyarwar addinin musulunci ce wanda ya zo cikin sunnan manzon Allah S.A.W.

Minstan ya ce abin takaci ne a kan irin sabanin da ake samu musamman a jihar Kwara wanda aka hana sanya hijabi a wata makaranta lamarin da ya haifar da zanga-zanga har aka rasa ran mutum guda cikin ɗaliban makarantar.

Mahukunta a makarantar Baptist High School sun nuna rashin goyon bayan saka hijabi a makarantar su wanda ƙungiyar kiristoci ta CAN ta goyi bayan su a kai.

Musulmi a jihar Kwara musamman na makarantar na kallon hakan a matsayin cin fuska tare da tauye musu wata dama da kundin taarin mulki ya basu har hakan ya sa su ka fita zanga-zanga a ranar Alhamis domin nuna rashin jin daɗinsu a dangane da matakin da hukumar makarantar ta ɗauka.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tsadar Karatu Na Iya Sa Rabin Ɗaliban Jami’a Su Gudu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta ce kashi 50% na ɗaliban da ke karatu na iya ajiyewa saboda tsadar karatu da ake ciki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodoke ne ya bayyana haka ya ce nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa ɗaliban da ke karatu a jami’o’in ƙasar kashi 50% daga ciki na iya ajiye karatun nasu.

A wata hira da aka yi da shugaban a gidan talabiji na Channels ranar Lahadi da daddare, ya gargaɗi ɓangaren ilimi na ƙasar da su farga a kan abinda ka iya faruwa.

Sai dai ya alaƙanta ƙara kuɗin da jami’o’i su ka yi da mafi ƙarancin albashin da ake biya na naira 30,000 a ƙasar.

Sannan ya ce akwai hatsari mai yawan gaske idan aka samu ƙarin matasa masu yawa da su ka bar makaranta.

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙarawa malaman jami’a albashi da kashi 30 ga masu matsayin farfesa.

Continue Reading

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: