Connect with us

Labarai

Dalilai Da Su Ka Sa ASUU Tafiya Yajin Aikin Wata Guda

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya sun fara yajin aikin gargaɗi na wata guda tun bayan gaza cimma matsaya da kuma rashin cika alƙawuran da su ka ce gwamnati ta ƙi musu.

Ƙungiyar ta sanar da tafiya yajin aikin bayan da ta shafe sama da mako guda ta na tattauna wa a kan yadda za ta fuskanci yajin aikin da ta shiga a halin yanzu.

Hukumar zartarwa a ta ƙungiyar ce ta sanar da shiga yajin aikin a yau Litinin wanda shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodeke ya sanar a Kegas.

Ƙungiyar ta buƙaci malaman jami’a su yi biyayya da umarninta na tafiya yajin aikin wanda su ke kallon hakan a matsayin hanyar za ta sanya gwamnatin ta waiwayi buƙatunsu.

Wasu daga cikin dalilan da ya sa ƙungiyar ta tafi yajin aikin su ne rashin biyansu albashinsu da alawu-alawus, da kuma rashin ƙarin girma ga waɗanda su ka cancanta sai kuma wasu gyare-gyare da kula da walwalar malaman.

A shekarar 2022 da mu ke ciki, wannan ne karo na farko da ƙungiyar ta fara yajin aikin duik da cewar ta sha tafiya yajin aikin a baya amma aka gaza cika musu burinsu.

Gwamnatin Najeriya ta sha zama da ƙungiyar domin yin sulhu amma har wa’adin da aka ɗauka ya cika ba a kai ƙarshen matsalar da ƙungiyar ke kokawa da gwamnati a kai ba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Gwamnatin Najeriya Za Ta Shawo Kan Barazanar Tsaro Da Jami’o’in Ƙasar Ke Fuskanta

Published

on

Ministan ilimi a Najeriya, Farfesa Tahir Mamman, ya jaddada yunkurinsa na tabbatar da ayyukan cigaba da za su daga likkafar bangaren ilimi a Najeriya.

 

Ya bayyana haka ne cikin wani jawabi da ya gabatar ga kwamitin mataimakan shugabannin jami’o’in Najeriya a Abuja yau Laraba.

 

Mamman ya tabbatarwa da wakilan cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu na da kyakkyawan yunkurin inganta harkokin koyo da koyarwa a daukacin jami’oin kasar nan.

 

Da yake nasa jawabin karamin ministan ilimi, Dr Yusuf Sununu, ya tabo batun matsalar rashin tsaro a jami’o’in Najeriya, wanda ya danganta batun da halin da ake ciki na garkuwa da aka yi da daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara.

 

Karamin ministan ya tabbatar da kyakkyawan yunkurinsu na kwararan matakai da aka dauka domin shawo kan al’amarin.

 

A cikin jawabinta, jagorar tawagar kuma shugabar kwamitin, Farfesa Lilian Salami ta nuna godiya da farin cikinta ga ministan bisa kasancewarsa mutum na farko a tarihi da aka nada minista lokacin da yake kan matsayin mataimakin shugaban jami’a.

 

Ms Salami ta hakaito wasu kalubale sa jami’o’in kasar ke fuskanta da su ka hadar da rashin isassun kudaden gudanarwa, wadatattun ma’aikata da sauransu.

Continue Reading

Labarai

Ba Mu Tura Kowa Ba Ya Gana Da ‘Yan Bindiga A Zamfara – Badaru Abubakar

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta magantu dangane da zargin da gwamna Zamfara Dauda Lawal Dare ya yi na sulhu da ƴan bindiga a jiharsa.

Ministan tsaro a Najeriya Badaru Abubakar ne ya ce sam gwamnatin ba ta wani shirin yin sulhu da ƴan bindiga kamar yadda gwamnan ya yi zargi.

Gwamnatin ta musanta zargin ne a yau bayan da gwamnan Zamfara ya zargesu da yin sulhu kuma hakan na iya zama mayar da Hakan na zuwa ne bayan da aka yi garkuwa da wasu ɗalibai na jami’ar tarayya ta Gusau a jihar a makon jiya.

Gwamnatin ƙasar ta ce ba ta sanya wata ƙungiya ko hukuma tattaunawa da ƴan bindiga ba, a don haka zargin ba gaskiya ba ne.

Sannan gwamnatin ta himmatu wajen kuɓutar da ɗaliban da aka sace, kuma ana samun kyakkyawans akamako.

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta ƙsar Attari Hope ya ce shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarni domin ganin an samar da kyakkawan sakamako wajen ceto ɗaliban.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Najeriya Ta Sanya Gobe Laraba A Matsayin Ranar Hutu Ga ‘Yan Kasar

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu ga ma’aikata na ƙasar.

Haka na ƙunshe a wata sanawar da ma’aikatar harkokin cikin gida babban sakataren ma’aikatar ya fitar ranar Litinin a madadin ministan.

Sanarwar ta ce an bayar da hutun ne domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam.

Gwamnatin ta buƙaci musullmi da su yi koyi da halayen Annabin tsira annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam musamman tausayi, jin ƙai, soyayya da haƙuri.

Sannan ta buƙaci ƴan ƙasar da su yi amfani da hutun wajen sanya ƙasar cikin addu’a musamman a kan harkokin tsaro da sauran al’amura.

Kuma gwamnatin ta buƙaci al’ummarta da su ci gaba da bai wa shugaba Bola Tinubu haɗin kai domin tabbatar da ayyukan ci gaba a ƙasar.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: