Connect with us

Labarai

Ƙungiyar Ɗalibai Ta Ƙasa Na Shirin Toshe Manyan Hanyoyin Najeriya

Published

on

Ƙungiyar ɗalibai a Najeriya NANS ta umarci mambobinta da ke jihohi 36 da babban binrin tarayya Abuja da su toshe dukkanin manyan hanyoyin zirga-zirga mallakin gwamnatin tarayya.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa Asefon Sunday ne ya sanar da haka a wata sanarwa da su ka sanya wa hannu shi da sakataren ƙungiyar.

Matakin ƙumgiyar na ƙasa ya biyo bayan yajin aikin da ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ASUU su ka tsunduma na wata guda bisa rashin cika musu alƙawuran da gwamnati ta yi musu tsawon lokaci.

Ƙungiyar ɗaliban ta ce matakin rufe manyan hanyoyin ya zo ne bayan matsayar da ƙungiyar ta cimma a yayin zaman da ta gudanar a jami’ar Sokoto.

Ƙungiyar ta ce yajin aikin malaman jami’an na mayar da ɗaliban baya tare da ja musu asara wajen biyan kuɗaɗen haya da sauran abubuwan da ɗaliban ke zamto musu asara a sanadiyyar yajin aikin.

Sanan ƙungiyar ta ce a ranar Litinin 28 ga watan da mu ke cki za ta yi gangami domin jan hankalin gwamnati na kawo ƙarshen yajin aikin baki ɗaya.

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta tafi yajin aikin wata guda domin nuna fushinsu a kan martaba bukatun da su ka miƙa wa gwamnatin tarayya.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Gwamnatin Najeriya Za Ta Shawo Kan Barazanar Tsaro Da Jami’o’in Ƙasar Ke Fuskanta

Published

on

Ministan ilimi a Najeriya, Farfesa Tahir Mamman, ya jaddada yunkurinsa na tabbatar da ayyukan cigaba da za su daga likkafar bangaren ilimi a Najeriya.

 

Ya bayyana haka ne cikin wani jawabi da ya gabatar ga kwamitin mataimakan shugabannin jami’o’in Najeriya a Abuja yau Laraba.

 

Mamman ya tabbatarwa da wakilan cewa shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu na da kyakkyawan yunkurin inganta harkokin koyo da koyarwa a daukacin jami’oin kasar nan.

 

Da yake nasa jawabin karamin ministan ilimi, Dr Yusuf Sununu, ya tabo batun matsalar rashin tsaro a jami’o’in Najeriya, wanda ya danganta batun da halin da ake ciki na garkuwa da aka yi da daliban jami’ar gwamnatin tarayya da ke Gusau a jihar Zamfara.

 

Karamin ministan ya tabbatar da kyakkyawan yunkurinsu na kwararan matakai da aka dauka domin shawo kan al’amarin.

 

A cikin jawabinta, jagorar tawagar kuma shugabar kwamitin, Farfesa Lilian Salami ta nuna godiya da farin cikinta ga ministan bisa kasancewarsa mutum na farko a tarihi da aka nada minista lokacin da yake kan matsayin mataimakin shugaban jami’a.

 

Ms Salami ta hakaito wasu kalubale sa jami’o’in kasar ke fuskanta da su ka hadar da rashin isassun kudaden gudanarwa, wadatattun ma’aikata da sauransu.

Continue Reading

Labarai

Ba Mu Tura Kowa Ba Ya Gana Da ‘Yan Bindiga A Zamfara – Badaru Abubakar

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta magantu dangane da zargin da gwamna Zamfara Dauda Lawal Dare ya yi na sulhu da ƴan bindiga a jiharsa.

Ministan tsaro a Najeriya Badaru Abubakar ne ya ce sam gwamnatin ba ta wani shirin yin sulhu da ƴan bindiga kamar yadda gwamnan ya yi zargi.

Gwamnatin ta musanta zargin ne a yau bayan da gwamnan Zamfara ya zargesu da yin sulhu kuma hakan na iya zama mayar da Hakan na zuwa ne bayan da aka yi garkuwa da wasu ɗalibai na jami’ar tarayya ta Gusau a jihar a makon jiya.

Gwamnatin ƙasar ta ce ba ta sanya wata ƙungiya ko hukuma tattaunawa da ƴan bindiga ba, a don haka zargin ba gaskiya ba ne.

Sannan gwamnatin ta himmatu wajen kuɓutar da ɗaliban da aka sace, kuma ana samun kyakkyawans akamako.

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta ƙsar Attari Hope ya ce shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarni domin ganin an samar da kyakkawan sakamako wajen ceto ɗaliban.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Najeriya Ta Sanya Gobe Laraba A Matsayin Ranar Hutu Ga ‘Yan Kasar

Published

on

Gwamnatin Najeriya ta ayyana gobe Laraba a matsayin ranar hutu ga ma’aikata na ƙasar.

Haka na ƙunshe a wata sanawar da ma’aikatar harkokin cikin gida babban sakataren ma’aikatar ya fitar ranar Litinin a madadin ministan.

Sanarwar ta ce an bayar da hutun ne domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam.

Gwamnatin ta buƙaci musullmi da su yi koyi da halayen Annabin tsira annabi Muhammad Salallahu Alaihi Wasallam musamman tausayi, jin ƙai, soyayya da haƙuri.

Sannan ta buƙaci ƴan ƙasar da su yi amfani da hutun wajen sanya ƙasar cikin addu’a musamman a kan harkokin tsaro da sauran al’amura.

Kuma gwamnatin ta buƙaci al’ummarta da su ci gaba da bai wa shugaba Bola Tinubu haɗin kai domin tabbatar da ayyukan ci gaba a ƙasar.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: