Connect with us

Labarai

Ƴan Sanda A Kaduna Sun Fatattaki Yan Bindiga A Babbar Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Published

on

Daga Khadija Ahmad Tahir

Kakakin ‘yan sandan jihar Kaduna ASP Muhammad Jalige shi ne ya bayyana cewa rundunar ta samu nasarar dakile harin a lokacin da ‘yan bindigan su ka yi nufin kai wa babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja hari.

Kakakin ‘yan sanda ya kara da cewa ‘yan sandan sun kai daukin ne a lokacin da su ka samu rahoto a kan harin inda su ka gano cewa ‘yan bindigan masu tarin yawa su na cikin kauyen Kurmin kare da ke karamar hukumar Chikum wanda ya ke kan hanyar Jihar Kaduna zuwa Abuja.

Kakakin ya ce ‘yan bindigan sun zo ne domin kai munanan hare-hare wasu gurare inda ba a san ko ina za su kai ba.

A yayin dakile harin ‘yan sandan sai da su ka yi musayar wuta da ‘yan bindigan daga bisani su ka fatattake su.

Muhammad Jalige ya tabbatar da kwato bindiga kirar AK 47 da harsasai masu tarin yawa.

Sannan jami’an na ‘yan sanda su ka bayyana cewa wasu daga cikin ‘yan bindigan sun jikkata.

Muhammad Jalige ya kara da cewa rundunar ‘yan sandan Jihar za ta cigaba da binciko bata garin a duk inda su ke domin magance su

Sannan ya yi kira ga mutanem da ke  kauyukan da su ke kusa da yankin da aka fatattaki ‘yan bindigan da zarar sun ji abinda basu gamsu da shi su yi gaggawar kai rahoto ga jami’an tsaro.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tsadar Karatu Na Iya Sa Rabin Ɗaliban Jami’a Su Gudu – ASUU

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta ce kashi 50% na ɗaliban da ke karatu na iya ajiyewa saboda tsadar karatu da ake ciki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar Frafesa Emmanuel Osodoke ne ya bayyana haka ya ce nan da shekaru biyu zuwa uku masu zuwa ɗaliban da ke karatu a jami’o’in ƙasar kashi 50% daga ciki na iya ajiye karatun nasu.

A wata hira da aka yi da shugaban a gidan talabiji na Channels ranar Lahadi da daddare, ya gargaɗi ɓangaren ilimi na ƙasar da su farga a kan abinda ka iya faruwa.

Sai dai ya alaƙanta ƙara kuɗin da jami’o’i su ka yi da mafi ƙarancin albashin da ake biya na naira 30,000 a ƙasar.

Sannan ya ce akwai hatsari mai yawan gaske idan aka samu ƙarin matasa masu yawa da su ka bar makaranta.

Idan ba a manta ba, a makon da ya gabata gwamnatin Najeriya ta ce ta ƙarawa malaman jami’a albashi da kashi 30 ga masu matsayin farfesa.

Continue Reading

Labarai

Gobara Ta Kama A Kotun Ƙoli Ta Najeriya A Abuja

Published

on

Rahotanni daga baban birnin tarayyar Najeriya Abuja na tabbatar da cewar kotun ƙoli ta kama da wuta.

Ofishin alƙalai uku aka ruwaito sun ƙone bayan tashin gobarar.

Godan jaridar Arise ya ruwaito cewar, wutar ta kama wai ɓangare na cikin kotun.

Sai dai ba a san sanadin tashin gobarar ba.

Wannan dai itace gobara da aka yi a kusa-kusa wadda ta shafi ofishin gwamnati.

Ko a watan Mayun shekarar da mu ke ciki, gobara ta kama a rundunar sojin samar Najeriya.

Yayin da a shekarar da ta gabata ta 2023 ma’aikatar kuɗi ta tarayya wani ɓangare ya kama da wuta.

Continue Reading

Labarai

Amuruka Ta Gargaɗi Ƴan Ƙasar Mazauna Najeriya Kan Ziyartar Wasu Jihohi Har Da Kano

Published

on

Ƙasar Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su kiyaye wajen ziyartar wasu jihohi da ka iya faɗawa cikin hatsari.

Sanarwar na zuwa ne bayan gudanar da wani bincike da su ka gano an samu ƙaruwar aikata manyan laifuka a jihohin.

Jihohin sun haɗa da Borno, Adamawa, Yobe, Kogi, Bauchi, Kaduna, Kano, Gombe, Bayelsa, Rivers, Enugu da jihar Bayelsa.

Sauran jihohin su ne Imo, SokOto, Zamfara, Katsina, da jihar Abia.

Ƙasar ta gargaɗi mutanenta da su kiyaye wajen ziyartar waɗannan jihohi domin su na iya faɗawa cikin tarkon masu garkuwa da mutane ko wasu miyagun laifuka.

Binciken da su ka yi sun gano cewar masu satar mutane domin neman kuɗin fansa na amfani da ƙarin mutane a wasu sassa domin cimma muradinsu.

Sannan gwamnatin Amurukan ta buƙaci ƴan ƙasar mazauna Najeriya da su ƙara sanya idanu a kan dukkanin zirga-zirgarsu don gudun faɗawa hatsari.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: