Connect with us

Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Ɗage Babban Taronta Na Ranar 26 Ga Wata

Published

on

Babbar jam’iyyar APC a Najeriya ta dakatar da babban taron da ta shirya gudanarwa a ranar 26 ga watan da mu ke ciki.

Dakatar da taron ya zo ne kwatsam bayan da uwar jam’iyyar ta ƙasa ta fahimci akwai rikice-rikice a cikin jam’iyyar a matakin jihohi da kuma shyya.

A wata wasika da shugaban jam’iyyar na  riƙo Maimala Buni ya sanyawa hannu a yau Litinin sun ce aun aikewa hukumar zaɓe ta ƙasa INEC domin sanar da ita halin da ake ciki.

Jam’iyyar ta nuna rashin daɗin faruwar hakan amma ta ce wannan ce hanya mafi sauki da za ta kawo ƙarshen rikice-rikicen da ke faruwa a cikin jam’iyyar.

Ko a jihar Kano ma jam’iyyar APC na fuskantqr kalubale a jihar Kano duk da cewar wata babbar kotu a Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyya ɓangaren gwamnan jihar a matsayin halastacce.

A nasu ɓangaren, tsagen shugabancin jam’iyyar wanda sanatan Kano ta stakiya Malam Ibrahim Shekarau ke jagoranta sun ce za su ɗaukaka ƙara a kan hukuncin da kotun ta yanke domin ba su gamsu da shi ba.

Click to comment

Leave a Reply

Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Zargi Gwamnatin Kano Da Almundahanar Kuɗaɗe

Published

on

Jam’iyyar APC da gwamnatin jihar Kano sun yi musayar yawu kan zargin wani shiri na karkatar da sama da Naira biliyan Takwas na kuɗin ƙananan hukumomin jihar.

Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas, a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata a Abuja, ya yi zargin cewa gwamnatin jihar na ƙoƙarin karkatar da naira biliyan 8,080,190,875.13.

A cewarsa rashin tabbas kan abin da zai kasance sakamakon hukuncin da kotun ƙoli ta yanke kan zaɓen gwamnan jihar ya sanya gwamnatin ɗaukar wannan matakin.

Shugaban jam’iyyar APC ya kuma gargadi ƙananan hukumomi da bankunan kasuwanci da su dakatar da shirin fitar da kuɗaɗen.

Jaridar Daily Trust ta ce da yake mayar da martani, kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Baba Halilu Dantiye, ya bayyana cewa.

Sannen abu ne cewa gwamnatin jihar Kano a ƙarƙashin ingantaccen shugabancin Injiniya Abba Kabir Yusuf, a cikin watanni bakwai da suka gabata ta yi suna wajen ganin an tabbatar da gaskiya da adalci da amfani da dukiyar al’umma yadda ya dace.

Ya kara da cewa gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ba za ta bari mutanen da ke jin zafi ba domin faɗuwa zaɓe kaɗai ba, amma saboda sun yi asarar hanyoyin satar dukiyar gwamnati su ɗauke mata hankali ba.

Continue Reading

Siyasa

Allah Ya Zaɓa Wa Al’ummar Kano Mafi Alheri A Kotun Ƙoli – Sanata Shekarau

Published

on

Tsohon gwamnan jihar Kano, Ibrahim Shekarau ya tofa albarkacin bakinsa game da shari’ar zaben da ake yi a kotun koli.

A wata zantawa da aka yi da shi, Sanata Ibrahim Shekarau ya ba gwamna Abba Kabir Yusuf da Nasiru Yusuf Gawuna shawara.

Babban ‘dan siyasar ya yi kira ga gwamna mai-ci da Nasiru Yusuf Gawuna da kotu ta ce shi ya lashe zabe da su koma Allah SWT.

Malam Shekarau ya bukaci ‘yan siyasar su roki zabin Ubangiji kuma su karbi duk kaddarar da ta auka masu bayan hukuncin kotu.

Rohoton na zuwa ne a daidai lokacin da ake jiran kotun koli ta yi hukunci karshe a shari’ar zaben gwamnan na jihar Kano.

Tsohon Ministan ilmin ya yi magana a Rumfar Afrika, ya ce abin da ya fi dacewa shi ne ayi addu’ar zabi mafi alheri ga mutanen Kano.

Shekarau wanda ya yi gwamna tsakanin shekarar 2003 da 2011 ya yi wannan addu’ar, sannan ya ce yana fatan APC da NNPP za su yi irin haka.

 

Continue Reading

Siyasa

Muna Da Ƙwarin Guiwar Samun Nasara A Kotun Ƙoli – Abba Kabir Yusuf

Published

on

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana kwarin gwiwarsa a game da hukuncin Kotun Koli.

Abba Kabir ya bayyana haka ne a jiya Lahadi 24 ga watan Disamba a filin wasa na Sani Abacha yayin bikin horas da matasa 2,500 a jihar.

Gwamnan ya yabawa alkalan kan yadda suka dage don ganin sun yi adalci kan shari’ar da ke gabansu.

Ya kuma yi kira ga jama’ar jihar da su kwantar da hankalinsu da kuma kara musu karfin gwiwa kan alkalan kotun.

Abba Kabir ya tabbatar wa magoya bayansa cewa ya na da tabbacin samun nasara a shari’ar da za a yanke.

Wannan na zuwa ne bayan da kotunan baya su ka soke nasararsa.

Gwamnan ya sake daukaka kara zuwa Kotun Koli inda a ranar Alhamis 21 ga watan Disamba ta zauna domin sauraron korafin

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: