Connect with us

Labarai

INEC Ta Kira Taron Gaggawa Bayan Sanya Hannu A Kan Sabuwar Dokar Zaɓe

Published

on

Bayan sanya hannu a kan sabuwar dokar hukumar zaɓe da aka sabunta wadda shugaban Najeiya Muhammadu Buhari ya saya wa hannu a jiya Juma’a hukumar zaɓe mai zaman kanta a Najeriya INEC ta kira mambobinta taron gaggawa domin tattaunawa a kan sabuwar dokar.

Kiran gaggawar ya zo ne bayan sanya hannu, kuma za su tattauna a kan sabuwar dokar da za ta taimaka wajen cimma sabbin tsare-tsare a yayin zaɓen 2023 mai gabatowa.

Kwamishinan zaɓe na ƙasa kuma shugaban kwamitin wayar da kai a kan al;amuran zaɓe Festus Okoye ne ya sanar da haka a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce sabuwar dokar ta ƙunshi sabbin cigaba wanda za a aiwatar da su a yayin zaɓen shekarar 2023 da ake tunkara.

Hukumar ta amince tare da yin farin ciki a kan sabbin stare-tsaren da aka samar wanda aka tabbatar za su taimaka wajen tsaftace zaɓe a Najeriya.

Sama da shekaru 10 aka shafe kafin gudanar da gyare-gyare na dokar zaɓe a Najeriya wanda a yanzu aka tabbatar da ita a shekarar 2022 da mu ke ciki.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Mutane A Fadar Sarki A Zamfara

Published

on

Wasu da ake zargi yan bindiga ne sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara.

 

Harin da su ka kai a jiya da daddare, sun lalata karfen sadarwa na kayin waya wanda hakan ya hana damar sadarwar a garin.

 

Yaan bindigan sun kai hari garin Dauran a ƙaramar hukumar Zurmi ta jihar

 

Mai magana da yawun ƴan sanda a jihar Yazid Abubakar ya tabbatar da faruwar hakan yau Alhamis.

 

Ya ce mutane uku aka kashe a garin yayin da aka yi garkuwa da wani mutum guda.

 

Sannan sun kone wata tashar sadarwar layin kira na MTN a garin.

 

Ƴan bindigan sun shiga garin dauke da muggan makamai.

 

Mazauna garin sun shaida cewar an kashe mutane uku sannan an yi garkuwa da wasu mutane da ba a kai ga ganosu yawansu ba a masarautar Zurmi.

 

A garin na Dauran kuwa, an yi garkuwa da mutane biyar

 

 

Continue Reading

Labarai

An Kama Masu Garkuwa Da Mutane Biyu Tare Da Dakile Wasu Hare-Hare A Sokoto, Kaduna Da Filato

Published

on

Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar kama wasu masu garkuwa biyu, yayin da au ka dakile wasu hare-hare a jihohin Sokoto, Kaduna da Filato.

 

Hakan na ƙunshe a wata sanarwa da su ka wallafa a shafinsu na X wato Twitter.

 

Su ka ce sun samu nasara ne a jiya Laraba.

 

Sanarwar ta ce sun tarwatsa ƴan bindigan a kauyen Sarma da ke Tangaza a jihar Sokoto.

 

Bayan wuta da su ka buɗe musu sun kuma babur, harsashi, da bindiga kirar AK47 guda ɗaya.

 

A wani cigaban kuma jami’an sun daƙile wani hari a hanyar ƙauyen Kasu da ke Kafanchan a karamar hukumar Jema’a a Kaduna.

 

A wannna waje ma sun kwato babur guda, harsashi da sauran makamai sannan su ka kama mutane biyu da su ke zargi masu garkuwa ne.

 

A wani farmakin da su ka kai a jihar Filato, a ƙaramar hukumar Barikin Ladi sun kashe ɗan fashi guda a shingen bincike da ke Kaskara.

 

 

Continue Reading

Labarai

An Sami Raguwar Yawan Haddura A Tituna Da kashi 42

Published

on

Hukumaar kiyaye afkuwar hadduta ta kasa aa Najeriya FRSC ta ce an samu raguwar haddura da kashi 42 la’akari da yadda ake samun hadduran a baya

 

Shigaban hukumar na ƙasa Dauda Biu ne ya bayyana haka a Abuja.

 

Ya ce mayar da hankali wajen tabbatar da bin kaidar tuki ya taimaka matuka wajen raguwar haddura da ake samu

 

A cewarsa, ko da a bikin salla karama da aka gaabatar a baya bayan nan,an samu raguwar haddura wanda hakan ya rage yawan mutanen da ke mutuwa.

 

Dangane da mutanen da ke mutuwa a lokutan bikin salla, an samu raguwarsu da kashi 52.5.

 

Yayin da aka samu raguwar mutanen da aka tseratar ba tare da rauni ba da kashi 43.8

 

Su kuwa mutanen da su ke samun rauni an samu ragi daa kashi 32.6, yayin da aka samu raguwar hadduran da kashi 42.5 la’akari da shekarar da ta gabata.

 

Sannan an samun raguwar masu karya dokokin tuki da kashi 14.5.

 

 

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: