Connect with us

Labarai

Jami’an Tsaro Sun Hallaka Yan Bindiga Sama Da 200

Published

on

Aƙalla ƴan bindiga sama da 200 jami’an staro su ka hallaka a jihar Neja.

An far wa ƴan bindigan ne a maɓoyarsu da ke dazukan Wushishi, Mokwa, da Lavun, sai ƙaramar hukumar Mariga duka a jihar Njea.

Kwamishinan al’amuran staro a jihar Emmanuel Umar ne ya sanar da haka wanda ya ce an ƙwato dabbobi da babura da saran abubuwan amfani daga hannun ƴan bindigan.

Ya ce an jikkata wasu da dama daga ƴan bindigan da jami’an staro su ka yi arangama da su sannan wasu daga cikin jami’an tsaro sun samu rauni yayin da biyu su ka rasa rayuwarsu.

Kwamishinan tsaro a jihar ya ce fafatawar ta faru ne tsakanin ranar Lahadi zuwa ranar Talata.

Ya ce an ƴan bindigan da aka hallaka yara ne ga Bello Turji, da Kacalla sai Kawajo da Yellow Jonbros, kuma an hallaka wasu daga cikin kwamandojin ƴan bindiga a jihar.

Yayin da mu ka zanta da guda mazauna garuruwan da aka kai musu hari a ƙaramar hukumar Kontogara, Abubakar ya shaida cewar ƴan bindigan sun sace shanunsa da na ƙaninsa fiye da 60 yayin da su ka kai wani hari.

Ya ce ƴan bindigan sun tare makiyayansu a ranar Asabar sannan su ka kwashe dabbobinsa da na kaninsa.

Ya kara da cewa akwai shanu takwas da su ka dawo daga cikin waɗanda ƴan bindigan su ka sace.

A ƙarshen makon da ya gabata ma sai da yan bindiga su ka shiga wasu ƙauyuka a ƙaramar hukumar Lavun tare da sace wasu amare bayan sun ƙaddamar da wasu hare-hare a ranarkun Asabar da Lahadi.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Zagon Kasan Da Kwankwaso Ya Yi Wa Jam’iyyar NNPP Ya Sa Ba Muyi Nasara A Kotuba- Alhaji Abbas

Published

on

Babban jigo a jam’iyyar NNPP, Alhaji Abbas Onilewura ya zargi dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso kan rasa nasarar jam’iyyar a jihar Kano.

 

A jiya Laraba 20 ga watan Satumba kotun ta yanke hukunci inda ta tsige Gwamna Abba Kabir na jam’iyyar a matsayin gwamna.

 

Kotun kuma ta tabbatar da Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben.

 

Yayin da ya ke martani kan hukuncin, Abbas ya ce Kwankwaso ya siyar da jam’iyyar lokacin da ya ke tattaunawa da APC kan mukamin minista a Abuja.

 

Onilewura ya bayyana haka ne a yau Alhamis 21 ga watan Satumba a cikin wata sanarwa da ya fitar.

 

Ya ce zagon kasa da Kwankwaso ya yi wa jam’iyyar ce ya jawo rashin nasararta a hukuncin kotun da aka yanke a jiya.

 

Ya kara da cewa Wannan rashin nasara babbar asara ce a jam’iyyar mu kuma hakan ya faru ne saboda son rai na Kwankwaso wanda ya siyar da jam’iyyar.

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Delta Ta Amince Da Rage Kaso 25 Na Kudin Jami’a A Jihar

Published

on

Gwamnatin jihar Delta ta amince da rage kashi 25 na kudin makarantar daliban jami’a a jihar.

Wannan dai wani bangare ne na tallafin da gwamnatin za ta bai wa daliban kuma ya shafi jami’a hudu mallakin jihar.

Hakan na kunshe a wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnan Festus Ahon ya sanyawa hannu ranar Laraba.

Sanarwar ta ce gwamnan ya bayar da umarnin bai wa ma’aikatan jihar tallafin naira dubu goma kowanne tsawon watanni uku.

Sannan an amince da kashe naira biliyan 5.522 ga ma’aikata 50,196 a matsayinalawus da aka yi musu karin matsayi.

Sannan gwamnatin za ta kashe naira biliyan goma wajen raba buhun shinkafa 17,000 da sama da buhu masara 60,000 ga marasa karfi.

Continue Reading

Labarai

Cibiyar Kare Hakkin Yan Jaridu Ta Yi Allah-Wadai Da Cin Zarafin Yan Jarida A Kano

Published

on

Cibiyar kare hakkin yan jarida ta duniya ta yi Alla wadai da cin zarafin yan jarida da wasu yan sanda su ka yi a Kano yau Laraba.

Salim Umar na jaridar Daily Trust da Zahradden Lawal na jaridar BBC an ci zarafinsu tare da lalata layan aikinsu yayin da us ke bakin aiki.

Babban jami’in kare hakkin yan jarida na duniya Melody Akunjiyan ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya aikewa manema labarai a yau.

Cibiyar ta ce abin takaici ne ganin yadda yan sandan su ka nuna rashin kwarewa ta hanyar cin zarafin yan jaridan yayin da su ke bakin aiki.

Cibiyar ta bukaci hukumar yan sanda ta kasa da su kula tare da kiyayewa a gaba wajen cin zarafin yan jarida musamman idan aiki ya hadasu da jami’an yan sanda.

Haka kuma cibiyar ta bukaci da aka ci gaba da bai wa yan sanda horo yadda za su dinga mu’amala da yan jarida tare da mutunta darajar dan adam.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: