Connect with us

Labarai

Kotu Ta Sauke Ƴan Majalisar Jiha 20 A Cross River

Published

on

Wata babbar kotu da ke zaune a Abuja ta sauke wasu yan majalisar dokoki ta jiha su 20 daga muƙaminsu bayan sauya sheƙa daga jam;iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC.

Ƴan majalisar dokokin jihar Cross River su 20 sun sauya sheƙa daga tsohuwar jam’iyyar su ta PDP zuwa jam’iyyar APC a shekarar 2021 da ta gaba.

Alƙalin kotun Justice Taiwo Taiwo a zaman kotun na yau ya sauke ƴan majalisun daga mukaminsu bayan sauya sheƙa da su ka yi daga jam’iyyar da aka zaɓe su a cikin ta.

Tun da farko jam’iyyar PDP ce ta shigar da kara gaban kotun inda ta buƙaci kotun ta sauke ƴan majalisar 20 daga muƙaminsu bisa sauya sheka daga jam’iyyar da mutane su ka zaɓe su a cikin ta.

Idan ba a manta ba jam’iyyar PDP ta shigar ta ƙara wasu  ƴan majalisar jihohi da na wakilai da wasu ƴan majalisar dattawa da gwamnan Zamfara a gaban kotu domin ganin an sauke su daga muƙamansu.

Jam’iyyar na ikirarin cewar muddin aka zaɓi mutum a cikin jam’iyyar to ƙuri’ar da aka zaɓe shi mallakin jam’iyyar ce don haka su ke buƙatar kotun ta sauƙe mutanen da su ka sauya sheƙa tare da maye gurbinsu da wasu da jam;iyyar ta amince da su.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Sheikh Ahmad Gumi Yayi Allah Wadai Da Kashe Al’umma Masu Taron Maulidi A Kaduna

Published

on

Fitaccen malamin addinin musulunci a Najeriya Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya yi Allah-wadai da hallaka mutane da jirgin soji yi a garin Tudun Biri a Jihar Kaduna.

Malamin ya bayyana hakan ne ta cikin wani jawabi da ya fitar a shafinsa na Facebook, Gumi ya ce lamarin abin takaici ne da ke yawan faruwa a yankin Arewacin Kasar.

Sheikh Ahmad Gumi ya kara da cewa ana maida Jihohin Arewacin Kasar tamkar zirin Gaza, kamar yadda sojojin Israila su ke hallaka mutanen kasar Falasdin.

A jawabin na Gumi ya zargi hukumomin Kasar da nufi mara kyau ga mutanen Kasar, tare da yin kisan kare dangi da ganganci ga al’ummar da ke kauyukan Arewa.

Gumi ya ce hakan ba zata taba yuwuwa ba jirgin yayi kuskure wajen sanya bam ga masu fararen kaya ba.

Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana cewa akwai wata a kasa wajen sanyawa masu taron mauludin bom din da jirgin yayi.

Continue Reading

Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayarwa Da Peter Obi Martani Akan Sukar Shugaba Tinubu

Published

on

Fadar shugaban kasa ta yiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party ga Peter Obi raddi akan yadda ya ke sukar gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Martanin ya fito ne daga ofishin Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ta bakin mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha a ranar Talata.

Sanarwar ta zargi Peter Obi da bata gwamnatin Tinubu bisa rashin nasarar da ya samu a lokacin zaben kasar.

Sanarwar ta ce Peter ya yi amfani da zargin zuwa taron COP na 28 da shugaban ya tafi da mutane 1411, domin cimma wata manufa tasa ta siyasa ta hanyar yaudara.

Sanarwar ta ce Obi ya shafe tsawon lokaci ya na sukar gwamnatin ta Tinubu domin ya nuna cewa ya na kishin kasa, kuma ba gaskiya yake fada ba a kalamannasa.

Martanin na zuwa ne bayan da Peter Obi ya soki gwamnatin tarayya akan kudin da aka kashe wajen zuwa taron dumamar yanayi na COP karo na 28 da kuma shirin gyara gidan mataimakin shugaban kasar Kashim Shettima.

 

Continue Reading

Labarai

Kar Gwamnatin Tarayya Ta Fara Tunanin Yafe Kisan Da Sojoji Suka Yiwa Mutane A Kaduna – Sheikh Yahaya Jingir

Published

on

Shugaban Majalisar Malamai na Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa’ikamatis Sunnah ta Kasa, Sheikh Muhammad Sani Yahya Jingir, ya bayyana cewa kada gwamnatin kasar ta fara batun cewa a yafe kisan da sojoji suka yi wa mutane a gurin taron Mauludi a Jihar Kaduna, domin Allah ya yi umarnin a hukumta dukkan wanda ya aikata irin haka.

Sheikh Yahya Jingir ya bayyana hakan ne yayin wani taron ganawa da manema labarai da ya yi a gidansa da ke garin Jos.

Jingir ya ce kisan gilla da aka yiwa mutanen abu ne wanda ba za a taba lamunta ba, kuma ba za a barshi haka ba, ba tare da an hukumta wadanda suka aikata aika-aika ba.

Shugaban ya kara da cewa dole ne a hukumta dukkan wanda aka samu da hanu akan lamarin,kisan mutanen da basuji ba su gani ba,kuma hakkin kowanne shugaba ne ya kare rayukan al’ummar da ya ke jagoranta.

Jirgin ya ce hukunta wadanda suka kashe mutanen da basuji ba su gani ba shine kyakkyawan shugabanci ga kowanne irin shugaba.

Ya ce Allah Ya haramta kisan bayin Allah, ko Musulmi ne ko Kirista ne ko wanda ba shi da addini ne, domin yana da daraja da ’yancin rayuwa, a wajen Allah.

Malamin ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta kafa kwararran Kwamitin bincike, wanda zai binciko musabbabin hallaka mutane.

Malamin ya yi kira da jami’an sojin da sauran hukumoomin tsaro a Kasar,da su dunga tsara yadda za su gudanar da ayyukansu kafin yi,domin kaucewa aikata ba dai-dai ba.

Daga karshe Malaman Jingir ya mika sakon ta’aziyarsa ga Sarkin Musulmi Alhaji Sa’ad Abubakar na lll da Sarkin Zazzau da gwamnan Jihar ta Kaduna da kuma ‘yan uwa da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a hari.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: