Connect with us

Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aikin Da Ta Ke Yi

Published

on

Ƙungiyar malaman jami’a a Najeriya ta sanar da janye yajin aikin gargaɗi da ta shiga.

Ƙungiyar ta sanar da hakan a shafinta na Tuwita.

Ƙungiyar ta ce malaman jami’a za su koma bakin aikinsu daga gobe Litinin sannan za ta ci gaba da duba yiwuwar tafiya yajin aikin sai baba ta gani a nan gaba.

Ƙungiyar ta shafe tsawon lokaci a yajin aikin, sai dai janye yajin aikin da su ka yi ba su yi wani karin bayani ko sun daidaita da ɓangaren gwamnati ba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Dola Ne Jami’an Tsaro Su Kara Kaimi A Kan Aikin Su-Tinubu

Published

on

Dole Ne Jami’an Tsaro Su Ƙara Ƙaimi A Kan Aikinsu – Tinubu

 

Shugaban kasar Najeriya Ahmed Bola Tinubu ya ja hankali ga manyan jami’an tsaro ƙasar da su kara himma da dagewa don Samun tabbataccen zaman lafiya a kasar.

 

Shugaban ya sanar da hakanne yayin ganawarsa da shugabanin hukomomin tsaron kasar karo na farko a fadarsa da ke Abuja.

 

Yayin ganawarsa da manaima labarai bayan kammala zaman mai bai wa shugaban kasar shawara kan harkokin tsaro yace shugaban sam ba zai lamunci yanayin da kasar take ciki ba.

 

Bola Tinubu ya ce bai dace kasar ta kara zama koma baya ba lokacin da sauran kasashen duniya ke ci gaba.

 

Ya kara da cewa wajibi ne a samu hadin kai tsakanin dukkanin sauran bangarorin tsaro ta fuskar tsaro.

 

 

 

 

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

CBN Ya Musanta Batun Karya Darajar Naira

Published

on

 

 

Babban bankin Najeriya (CBN) Ya musanta wata sanar wa da ta fita kan cewa darajar Naira ta karye a hukumance.

 

Hakan ya fito ne ta bakin Mukaddashin Daraktan bankin Abdulmuminu,

Abdulmuminu, yace ko a jiya Laraba an siyar da dala ɗaya a kan naira 465.

 

Ya kuma kara da cewa Rahoton da ya fita kan sanarwar karyewar darajar Naira ba gaskiya ba ne.

 

Bankin ya shawarci Mutane da su yi watsi da Rahoton da su ka ji kan karyewar darajar Nairar.

 

 

 

 

Continue Reading

Labarai

Mutane 7 Sun Rasu A Wani Hatsari Da Auku A Bauchi-FRSC

Published

on

Hukumar kiyaye hadurraya kasa FRSC ta ba bayyana cewa mutane takwas ne suka rasu bayan da wani hatsari ya auku a jihar Bauchi.

 

Kamar yadda hukumar ta kiyaye hadurra ta bayyana ta ce hatsarin ya faru ne akan babbar hanyar Darazo zuwa Bauchi ajiya Laraba 31 ga watan mayu.

 

Ta ce hatsarin ya faru da misalin karfe 1:43 na rana inda bayan haduwar motar kirar Hilux da kuma wata motar daukar fasinja Golf.

 

Sannan hatsarin ya rutsa da mutane 14 mata bakwai maza bakwai inda maza hudu suka rasu da mata hudu ciki harda yara kanana.

 

Sannan akwai wadanda suka Samu raunuka a jiki.

 

Sai dai kamar yadda hukumar ta kiyaye hadurra ta bayyana ta ce ta mika sauran masu rauni izuwa asibitin Darazo.

 

A ko da yaushe hukumar kiyaye hadurran ta na bayyana cewa direbobi su guji gudun wuce kima duba da yanayin damina ne a yanzu.

 

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: