Connect with us

Labarai

Za Mu Bai Wa INEC Cikakken Goyon Baya Don Gudanar Da Sahihin Zaɓe – Buhari

Published

on

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sake tabbatar da cewar gwamnatinsa ta bai wa hukumar zabe mai zaman kanta a Najeriya INEC cikakken goyon baya domin gudanar da zabe cikin na gaskiya da adalci a shekarar 2023.

Shugaban ya kuma baiwa INEC tabbacin samun ‘yancin kai, yana mai cewa bayan kammala zaben fidda gwani na jam’iyyun siyasa, yanzu idanunsu sun karkata ga zaben shekarar 2023 a Najeriya.

Shugaba Buhari, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar a daren Laraba, ya ce shugaban ya bayyana haka ne yayin wani taro da wakilan ‘yan Najeriya mazauna kasar Portugal.

Ya ce suna kuma sa ran samun nasarar mika mulki ga gwamnati mai zuwa, Kamar yadda ya sha fada a baya, gwamnatinsu ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yin abubuwan da suka dace da kuma jin dadin ‘yan Najeriya na gida da waje.

Buhari wanda ya ba da misali da zabukan gwamnoni da aka gudanar a jihohin Anambra da Ekiti, ya ce gwamnatinsa za ta tabbatar da cewa ba ta da hurumin yin katsalandan a zabe tare da dagewa cewa a bar ‘yan Najeriya su zabi jam’iyya da dan takarar da suke so.

Shugaban ya yi gargadin a guji amfani da kafafen sada zumunta wajen cin mutunci da tunzura jama’a.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ma’aikatan Filayen Jirgin Sama A Najeriya Za Su Haramtawa Jirage Tashi A Najeriya

Published

on

Ƙungiyoyin ma’aikatan jiragen sama na Najeriya sun yi barazanar rufe dukkan filayen sauka da tashin jiragen sama na Kasar daga ranar 31 ga watan Maris din nan da muke ciki.

Ma’aikatan sun yi barazanar rufe filayen jiragen Kasar ne, tare da nema gwamnatin tarayya da ta dauki matakin kora ga jami’in hukumar hana fasa kauri ta Kasa kwastam da ake zargi da hannu wajen cin zarafin daraktan tsaro a hukumar kula da filayen jiragen sama ta Kasa.

A wata sanarwa da gamayyar kungiyoyin suka fitar sun nuna rashin aminta da abin jami’in na Kwastom ya aikata.

Sannan kungiyoyin sun kuma nuna rashin jindadunsu bisa yadda ake samun yawaitar cin zarafin ma’aikatan hukumar kula da filayen jiragen saman Kasa.

A Bangaren hukumar ta kwastam ta ce rashin fahimtar da ya faru tsakanin jami’inta da Ma’aikatan filin sauka da tashin jiragen sama na Murtala Muhammed da ke Jihar Legas ya ce rashin fahimta ne.

Mai magana da yawun hukumar na Kasa Abdullahi Mai Wada Aliyu ya ce hukumar na kokarin ganin ta hada kai tsakanin bangaren, don ci gaba da gudanar da aiki yadda ya kamata.

Continue Reading

Labarai

INEC Ta Ki Amince Da Bukatar Yiwa Sanata Natasha Kiranye

Published

on

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC Hukumar INEC ta ki amincewa da bukatar neman tsige Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, bisa rashin rubuta adireshinsu, lambobin wayarsu, ko kuma gmail din a cikin wasikar da suka aikewa da hukumar.

INEC ta ki amincewa da bukatar ne ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Talata, mai dauke da sa hannun kwamishinan hukumar Sam Olumekun.

Sanarwar ta ce bayan mika bukatar yiwa Sanata Natasha kiranye da ‘yan Mazabarta su ka yi ga hukumar, sun gudanar da zama akan batun a taron da saba gudanarwa Mako-mako.

Hukumar ta kara da cewa hanyar dakatar da dan majalisa na cikin kundin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999, da dokar zaɓe ta shekarar 2022 da ta gabata da kuma ka’idojin hukumar na shekarar 2024.

Hukumar ta ce takardun korafe-korafen da ake kai’wa hukumar daga yankin na Kogi ta Tsakiya na hade da jakunkuna shida na takardu da aka bayyana na dauke da sa hannun sama da rabin masu zabe 474,554 ne daga rumfunan zaɓe 902 a yankunan rajista 57 da ke cikin kananan hukumomin Adavi, Ajaokuta, Ogori Magongo, da kuma Okehi da Okene.

Hukumar ta bayyana cewa wakilan masu shigar da korafi ba su cika dukka wata ka’idoji da ake bukata ba wajen yiwa dan Majalisar kiranye ba.

Sanarawar ta ce Adireshin da aka sanya a cikin takardar shi ne Okene a jihar Kogi, wanda ba tare da bayyana cikakken guri ba da za a iya tuntuɓarsu, sannan sun kuma bayar da lambar waya ta babban jagoran masu ƙorafi kadai maimakon lambobin dukan wakilan masu ƙorafi.

Hukumar ta ce da zarar an cika dukkan sharruddan Korafi tare da bin ka’idojin, hukumar za ta fara guanar da tantance sa hannun a rumfunan zaɓe ta hanyar tsari na buɗe ido da zababbun masu ƙorafi kadai za su shiga.

Acewar Hukumar za ta bi dukkan doka wajen tantance dukkan korafe-ƙorafen da ake aikawa hukumar.

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Riko Na Rivers Ya Nada Sakataren Gwamnatin Jihar

Published

on

Gwamnan riko na Jihar Rivers Ibok-Ete ya nada Farfesa Ibibia Lucky Worika a matsayin sabon Sakataren gwamnatin Jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka fitar daga fadar gwamnatin Jihar a yau Talata.

Sanarwar ta bayyana cewa nadin Lucku ya biyo bayan yin nazari kan ƙwarewa da gogewarsa a bangarori daban-daban.

Sanarwar ta kuma ce nadin Worika ya kuma yi daidai da manufarsa ta amfani da kwararru daga jihar Rivers domin samar da tabbataccen zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jihar.

Nadin Sakataren na kuma zuwa ne a daidai lokacin da gwamnan rikon ya amince da yin murabus din Shugaban Ma’aikatan gwamnatin Jihar George Nwaeke.

Inda kuma gwamnan rikon ya nada Iyingi Brown wanda ya kasance babbar sakataren ofishin shugaban Ma’aikatan Jihar, inda kuma zai zauna a matsayin mai rikon mukamin shugaban Ma’aikatan har zuwa lokacin da za a nada wani sabon shugaban Ma’aikatan.

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: