Wasu ‘yan bindiga sun saki wasu mutane 12 da su ka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna.

Kafin sako mutanen ‘yan bindigan sun karbi buhun shinkafa 20 da buhun Wake 20 jarkar Man gyada Jarkar Manja da kuma katin waya harna naira 10,000 a matsayin fansar mutanen da su ka sace.

Rahotanni sun bayyana cewa ‘yan bindigan sun hallaka wani Manomi tare da yin garkuwa da mutane 20 a cikin gonakinsu da ke yankin Jangali da kwada duk da ke cikin yankin na Birnin gwari.

Kungiyar ci gaban masarautun Birnin Gwari BEPU ce ta bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar ta hannun shugaban kungiyar Ishak Usman Kasai a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ce a baya ‘yan bindigan sun nemi naira 12 a matsayin kudin Fansar wasu manoma da su ka yi garkuwa dasu.

Leave a Reply

%d bloggers like this: