Wasu batagarin matasa a Jihar Borno sun kaiwa tawagar motocin gwamnan Jihar ta Borno Babagana Umara Zulum hari a garin Maiduguri da ke Jhar.

 

Masanin tsaro a yankin tafkin Chadi Zogazola Makama ya bayyana cewa lamarin ya farune a yammacin ranar Alhamis.

 

Makama ya rawaito cewa matasan sun kaiwa tawagar gwamnan harin ne a lokacin da ya ke kan hanyar sa ta dawowa daga mahaifar sa Mafa da ke Jihar.

 

Zogazola ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter,inda ya ce koda a makwannin da su ka gabata sai da aka kaiwa tawagar matar gwamnan hari Hajiya Fatima Zulum a Dalori da ke cikin karamar hukumar Konduga da ke Jihar inda aka lalata mutoci takwas.

 

Makama ya kara da cewa matasan da ke unguwar Kaleri a Maiduguri ne su ka yi aika-aikar inda su ka lalata motocin tawagar uku.

 

Wata majiya ta bayyana cewa motocin da aka lalata sun hada da motar injiniyoyi manema labarai tare da wata mota guda daya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: