Kungiyar kwallon kafa ta Manchester United ta cire dan wasanta Anthony Matial a cikin tawagar da za ta fafata wasan karshe na kufin FA .

Kamar yadda kungiyar ta fitar a jiya Talata ta ce dan wasan Matial ya samu rauni don haka ba zai samu damar bugawa kungiyar wasa ba.

Dan wasan na Faransa wato Anthony Jordan Matial ya na da shekaru 27 sannan ya fafata wasanni kimanin 162 a Manchester United tare da cin kwallaye 62 tun bayan zuwansa Man United daga Manaco shekarar 2015.

Wasan Wanda ake saran fafatawa a ranar Asabar Wanda da kungiyar kwallon kafa ta Manchester City shi ne wasan karshe don daukar kofin FA a kasar Birtaniya.

A makon da yagabata ne ranar Lahadi Man United ta doke Fulham da ci 2-1 a gasar.
Sannan ana saran fafatawar da Man City a ranar Asabar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: