Connect with us

Labarai

Ƙungiyoyi Masu Zaman Kansu Sun Goyi Bayan Ganduje Don Zama Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

Published

on

Kungiyar Progressive Union of Southern Nigeria (PUSSON), kungiyoyi masu zaman kansu sama da 50 daga dukkan shiyyoyin siyasa uku na Kudancin Najeriya, sun taya tsohon gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje (CON), murnar samun nasarar goyon bayan shugaba Bola Tinubu tare da sauran masu ruwa da tsaki domin ya zama shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa.

 

A wata wasika da aka hada hannu da Kodinetan kungiyar, Mista Frank Idowu Dele da Sakatariyar, Misis Grace Okechukwu kuma suka mika wa Ganduje, ‘yan mintoci da suka gabata, sun bayyana jin dadinsu da fitowar sa tun da farko.

 

A cewar wasikar, zaben Ganduje na zama shugaban jam’iyyar shaida ne karara kan yadda tsohon gwamnan ke da amana da biyayya ga shugaba Tinubu da tsarin siyasar jam’iyyar.

 

Da yake jaddada cewa, fitowar Ganduje zai taimaka wa dimokuradiyyar cikin gida da kuma zurfafa sanin siyasa a cikin jam’iyyar, domin ci gaban siyasar kasa baki daya.

 

Ya kara da cewa, “A cikin wannan lokaci da jam’iyya mai mulki ke fama da rikici, lokacin da shugaban jam’iyyar na kasa da Sakatariyar jam’iyyar suka yi murabus, abin da jam’iyyar ke bukata shi ne wanda yake da gogewa a fagen siyasar jam’iyya, dimokuradiyya da kuma kyakkyawan alaka ga kowa.

 

Wasikar ta ce, lokacin da al’amura suka yi tsauri, ana bukatar gaskiya da amana, mai girma gwamna an bayyana cewa ya zama daya daga cikin amintattun jam’iyyar da za su dace da wannan mukami.

 

Da suke jinjina wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, saboda zurfin tunani da fahimtar da Ganduje yake da shi a fagen siyasar jam’iyya, sun ce, sauyin mai girma Gwamna ya nuna yadda Nijeriya da jam’iyya mai mulki musamman ke shirin saka masa da kishin kasa, sadaukarwa, jajircewarsa da rashin son kai.

 

Sun tuno da yadda yankin Kudancin kasar nan suka amince da shi, tun kafin yanzu, kishin Ganduje da jajircewarsa wajen gina kasa da hadin kan kasa ya ce suna iya tunawa da yadda suka ceto Najeriya daga fadawa cikin rudani a lokacin da suka sasanta tsakanin kungiyoyin Arewa da Igbo.

 

Sun ba da tabbacin cewa jam’iyyar APC mai mulki za ta samu dimbin nasarori daga dimbin gogewar da ya yi, da salon siyasarsa, da biyayyar sa ga jam’iyyar da kuma zurfin fahimtarsa ​​da fahimtar juna a cikin kasa.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.

An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.

Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

Published

on

A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Continue Reading

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.

Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: