Labarai
Karota Ta Buƙaci Hukumar Shige Da Fice Ta Horas Da Jami’anta


Hukumar kula da Shige da Fice ta Ƙasa shiyar Kano (Nigerian Immigration Service) ta sha alwashin haɗa hannu da Hukumar kula da zirga zirgar ababen Hawa ta Kano (KAROTA) wajen dakile shigowar baƙi Jihar Kano ta tashoshin Motoci ba bisa Ƙa’ida ba.

Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa a jihar Kano Ahmad Dauda Bagari ne ya sha wannan alwashi yayin da ya karbi baƙuncin sabon Shugaban Hukumar (KAROTA) Engr. Faisal Mahmud Kabir a ofishinsa.
Bagari ya ce Hukumomin guda biyu tamkar Ɗan’juma ne da Ɗanjimmai wajan gudanar da ayyukansu.

Dauda Bagari ya ce ƙofar Hukumarsa (Nigerian Immigration service) a buɗe take wajen ganin an gudanar da aiki kafaɗa-da-kafaɗa da Hukumar (KAROTA) domin ciyar da jihar Kano gaba dama kasa baki ɗaya gaba.

Yana mai cewa Hukumarsa a shirye take wajen kula, tare da kama baƙin haure waɗanda suke zuwa ƙasar nan ta hanyar tashoshin mota ba bisa ƙa’ida ba.

A nasa jawabin Shugaban Hukumar KAROTA Engr. Faisal Mahmud Kabir ya ce Hukumar KAROTA a shirye take wajan gudanar da aiki tare da Hukumar kula da Shige da ficen.
Yana me cewa ya kai ziyarar ce domin sada zumunci da kulla alakar aiki duba da yadda ayyukan Hukumar ke da alaka dana Hukumar KAROTA, a don haka a shirye muke domin gudanar da aiki tare da nufin ciyar da harkar sufuri a fadin jihar nan gaba ɗaya.
A ƙarshe ya roƙi Hukumar da ta taimaka wajen bayar da horo ga jami’an KAROTA domin su gane baƙin haure waɗanda suka shigo jihar Kano ba bisa ka’ida ba.
Labarai
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba


Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.
An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.
Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.
Labarai
Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa


A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.
A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.
Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.
Labarai
Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba


Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.
Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.
-
Mu shaƙata10 months ago
Kun San Ma’anar Kalmar Chiza Dani? Waƙar Da Ke Tashe A Kwanakin Nan?
-
Al'ada5 years ago
Fahimta ta a kan matsalar aure a ƙasar Hausa
-
Labaran ƙetare5 years ago
Wajibi ne duk wani namiji ya Auri mata Biyar ko a ɗaure shi a gidan yari— Sarkin Swaziland
-
Labarai5 years ago
Ba kwaya ƴan sandan kano suka kama ba, babu sinadarin maye a cikin maganin – NAFDAC
-
Addini3 years ago
Lokutan da ake saurin karɓar addu’a
-
Bidiyo3 years ago
Wanene Halilu Ahmad Getso? Ƴar cikin Gida
-
Lafiya5 years ago
Menene Genotype ? Amfanin yinsa kafin Aure – Mujallar Matashiya
-
Labarai8 months ago
Akwai Jihohi Goma Da Zaɓen Gwamna Bai Kammala Ba A Najeriya Ko Har Da Kano?