Connect with us

Labarai

Abubuwan Da Su Ka Faru Yayin Zanga-Zanga A Kano Da Abuja

Published

on

Najeriya

A yau Laraba kungiyar kwadago ta gudanar da yajin aiki da zanga-zanga a fadin Najeriya.

 

Kungiyar ta gudanar da yajin aikin ne sakamakon matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa da ake fuskanta.

 

An yi wa yajin aikin take da A Bar Talata Ya Shaki Numfashi.

 

Tun a baya kungiyar ta shirya tafiya yajin aikin bayan ƙarin kudin man fetur da aka samu a kasar.

 

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ne ya ayyana dakatar da cigaba da bayar da tallafin man fetur a Najeriya jim kaɗan bayna rantsar da shi a matsayin sanon shigaban ƙasar Najeriya.

 

Jihohi 36 sun fito tare da yin tattaki na zanga-zangar lumana, da nufin jan hankalin gwamnati donmin duba halin da ake ciki.

 

Kungiyar ta ce akwai bukatar a yi duba n atsanaki a kna lamarin, ganin yadda ma’aikata a Najeriya ke batar da kashi 70 na albashinsu a hanyar sufuri.

 

 

 

Kano

Kungiyar kwadago a jihar Kano ta gudanar da yajin aiki tare da zanga-zangar lumana a yau Laraba.

 

Jihar Kano ta bi sahun jihohin Najeriya wajen yin tattakin da kungiyar kwadago ta kasa ta shiya yi domin jan hankalin gwamnati a kan matsin rayuwa da ake ciki.

 

Shugaban ƙungiyar na jihar Kwamared Kabiru Inuwa ya yi karin haske wanda ya nuna gamsuwa a kan matakin da su ka ɗauka.

 

Ya ce ƙungiyar ta gamsu da matakin da aka ɗauka kuma haakan yayi tasiri donin yaa sanya gwamnatin ta waiwayi halin da aake ciki sabanin baya.

 

Ya kara da cewa kungiyar na da mataki daban-daban kuma wannan shi ne na farko sannan za su sake zama domin duba matakin da ya dace su dauka a gaba.

 

 

Abuja

Masu zanga-zanga a birnin tarayya Abuja sun ɓalle kofar shiga majalisar dokoki ta ƙasa tare da mamaye haaraba.

 

Hakan ya faru yayin da su ka fita don yin zanga-zangar lumana hadi da yajin aiki sakamakon tsadar man fetur da kungiyar ta ce ba ta gamsu da shi ba.

 

Mutane da dama sun yi cincirindo a harabar majalisar tare da kira ga gwamnati na ganin an duba halin da ake ciki wajen samar da saukin rayuwa a Najeriya.

 

Bayan gwamnati ta yi yunkurin raba naira biliyan 500 ga marasa galihu a kasar don rage radadin cire tallafin man fetur, kungiyar ta yi watsi da batun.

 

Idan ba a manta ba shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi wa yan Najeriya jawabi a kan haalin da ake ciki har ma yaa yabawa kamfanoni masu zaman kansu da su ke tallafawa kasar wajen daukar mutane aikin yi.

 

Sannan ya ce za a yi amfani da kudaden wajen bayar da tallafi, samar da motocin sufuri da kuma amfani da kudin don farfado da bangaren ilimi ta yadda kowanne dan ƙasa zai smau ilimi ba tare da samun targaro a kan kudi ba.

 

Jawabin shugaban ya janyo cece ku ce a bakin al’umma wanda wasu ke ganin hakan ba zai wadatar ga yan kasar ba.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.

An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.

Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

Published

on

A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Continue Reading

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.

Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: