Connect with us

Labarai

‘Yan Sanda A Zamfara Sun Dakile Wani Harin ‘Yan Bindiga A Jihar

Published

on

Rundunar jihar Zamfara ta yi nasrara daƙile wani harin ƴan bindiga tare da kama wata da take kai musu bayanai.

Mai magan da yawun ƴan sandna jihar ASP Yazid Abubakar ne ya bayyana haka ranar Juma’a a Gusau babban birnin jihar.

Ya ce jami’an su sun samu nasarar daƙile harin bayan shirin ƴan biindiga na kaiwa wani yanki a ƙaramar hukumar Zurmi a jihar.

Ya ce sun yi musayar wuta na tsawon awanni kafin daƙile harin na ƴan bindiga yayin da su ka kai musu hari ofishinsu da ke Zurmi a jihar.

A sakamakon haka sun samu nasarar kama guda daga ciki yayin da sauran su ka tsere ɗauke da raunin haribin bindiga a jikinsu.

Ƴan sandan sun kama wata mace mai shekaru 35 mazauniyar garin Rukudawa da ake zargi da kaiwa yan bindiga bayanai kuma tuni su ka ffara bincike a kanta.

Kakakin yan sandan jihar ya ce matar ta bayyana musu cewar ta kasance ta na aiki ne da ƴan bindigan ƙarƙashin jagoransu Ɗanƙarami.

Ƴan sandan sun kwato bindigu ƙirar AK47 guda biyu tare da babur, wayoyin hannu da harsashi kuma su na ci gaba da bibiyar don kama waɗanda su ka tsere.

Sannan a ranar 27 ga watan Yuli da ya gabata ƴan sanda sun kama wasu mutane biyu da ake zargi ƴan bindiga ne a yankin Saminaka da ke ƙwaryar binin Gusau babban birnin jihar.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

‘Yan Takarar Gwamnoni A Jam’iyyar PRP Sun Koma SDP

Published

on

‘Yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PRP a zaben 2023 na sun sauya sheka zuwa jam’iyyar SDP.

Shugaban kungiyar ‘yan takarar gwamnan a PRP Malam Hayatuddeen Lawai Makarfi ya tabbatar da ficewarsu daga PRP zuwa SDP.

Shugaban kungiyar ya bayyana cewa sun dauki matakin koma SDP ne domin tsamo kasar nan daga halin da take ciki.

Lawai Makarfi wanda ya yi takarar gwamna a jam’iyyar ta PRP a Jihar Kaduna, ya bayyana cewa mutane na sauya sheka zuwa SDP ne bisa yadda da shugabancinta.

Makarfi ya ce sauya shekar su wani shiri ne na hadin domin kubtar da Najeriya daga shugabanci mara kyau, inda kuma ya nuna damauwarsa bisa yadda ake ci gaba da samun zubar jini, karuwar takauci, ya yin da hukumomin gwamnati ke durkushewa, inda kuma jam’iyyar APC da PDP suka mayar da mulkin kasar tamkar kasuwanci.

Kungiyar ‘yan takarar gwamnan ta kuma mika godiyarta ga PRP bisa damar da ta ba su a siyasa, inda suka ce a halin yanzu sun koma kan hanyar gaskiya.

Shugaban jam’iyyar SDP Malam Shehu Musa Gabam ya shaida musu cewa jam’iyyar za ta bai’wa masu sauya shekar dukkan wata dama da ta kamata.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya Sama 1,000

Published

on

Gwamnatin Kaduna Jihar ta amince da daukar ma’aikatan lafiya 1,800 a fadin Jihar.

Kwamishiniyar lafiya ta Jihar Hajiya Umma Ahmad ce ta tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis.

Sanarwar ta ce gwamnatin Jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Uba Sani za a dauki Ma’aikatan ne domin cike gurbin Ma’aikatan a dukkan cibiyoyi kiwon lafiya matakin farko na Jihar.

Sanarwar ta kara da cewa daukar Ma’aiktan hakan zai kara tabbatar da ci gaban Jihar akan matsayin da ta ke dashi a fannin kiwon lafiya matakin farko a Najeriya.

Kwamishinyar ta kuma ce daukar ma’aikatar zai kawo karshen karancin ma’aikata da ake samu a cibiyoyin kiwon lafiyar, tare da raguwar yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da kananan yara, da kuma kara inganta lafiyar mutanen Jihar.

Acewarta a halin yanzu ana ci gaba da gyaran cibiyoyi 255 na kiwo lafiya matakin farko, yayin da za a daga martabarsu zuwa mataki na biyu, da samar da kayan aiki na zamani, tare da bayar da muhimman magunguna duk a kokarin da gwamnatin Jihar ke yi na inganta bangaren kiwon lafiya.

Kwamishinar ta kuma ce cibiyoyin za su dunga aikin duba masu cutuka daban-daban da suka hada da ciwon suga da bai yi karfi ba, hawan jini shima da bai yi karfi ba, da bayar da tallafin wajen haihuwa da dai sauransu.

Continue Reading

Labarai

Majalisar Wakilan Za Ta Haramtawa Masu Shekaru Sama Da 60 Tsayawa Takara

Published

on

Majalisar wakilan Najeriya ta tsallake karatu na biyu kan kudurin da zai haramtawa ‘yan takarar shugaban Kasa, da na gwamnan masu shekaru sama da 60 tsayawa takara.

A zaman Majalisar na yau Alhamis, da kudurin ya tsallake karatu na biyu, bayan da dan Majalisar Hon Ikeagwuonu Ugochinyere ya dauki nauyin kudurin da ke bukatar canza wasu bangarori na kudin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999.

Rahotanni sun bayyana cewa da zarar kudurin ya tsalle karatu na uku, kuma shugaban Kasa ya sanya hannu akansa, hakan zai sauya fasalin tsayawa takara a Kasar.

Daga cikin abubuwan da kudurin ya kunsa sun hada da, dukkan wanda ya haura shekaru 60 da haihuwa b azai tsaya takarar shugaban Kasa ba, ko gwamna a Kasar.

Sannan kuma wajibi dukkan dan takara ya kasance ya mallaki shedar digirinsa na farko a bangaren da ya fi kwarewa akai, a matsayin mafi karancin takardar karatu.

Ya yin da kuma kudin ya bukaci yin gyara a sashe na 131 na kudin tsarin mukin Kasa, na bukatar iyaknce shekaru ga kowanne dan takarar shugaban Kasa, tare da sashi na 177 ga gwamomin Jihohi.

Baya ga wannan kuduri majalisar ta kuma amince da wasu kudurori daban-daban da suka shafi ci gaban Najeriya.

 

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: