Connect with us

Labarai

Karota Za Su Cigaba Da Kama Masu Tuƙa Adaidaita Sahu Ƴan Ƙasa Da Shekara 18

Published

on

 

Hukumar kula da Zirga-zirga Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta ce zata ci gaba kama yaran da shekarunsu bai kai 18 ba waɗanda suke tuƙa Baburin Adaidai Sahu.

A wata sanarwa da kakakin hukumar Nabulisi Abubakar K/Naisa ya sanyawa hannu, ya ce Shugaban Hukumar KAROTA Engr Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka, lokacin da yake karbar baƙuncin gamayyar ƙungiyoyin Adaidai Sahu na jihar nan, ƙarƙashin jagorancin Alh. Mansur Tanimu

Engr. Faisal ya ce Hukumar KAROTA ba za ta lamunci bawa ƙananan yara wandanda shekarunsu bai kai 18 ba tuka Adaidai Sahu

Haka kuma, Hukumar ba za ta yadda da yin amfani da waya a lokacin tuki ba, da kuma ɗaukar kayan da suka wuce kima a cikin Adaidai Sahu

A nasa jawabin Shugaban Gamayyar Ƙungiyar Adaidaita Sahu ta jihar Kano Alh. Mansur Tanimu ya ce sun zo Hukumar KAROTA ne domin taya murna ga sabon shugaba tare da alkawarin bayar da haɗin kai domin ciyar da jihar Kano ta ɓangaren sufuri gaba

Ya bayar da tabbacin bawa Hukumar KAROTA haɗin kai domin ciyar da jihar Kano gaba

A wani cigaban kuma, shugaban Hukumar ya karɓi baƙuncin kungiyar Adaidai Sahu ta Kwankwasiyya kar ƙarƙashin jagorancin Comr. Nazifi BK Gidan Kuɗi,

Sun roƙi Gwamnatin jihar Kano ta samar da makaranta wadda za ta dinga bayar da horo ga matuƙa Baburan Adaidai Sahu na faɗin jihar nan hakan zai taimaka wajen rage yawan aikata laifukan tuki titinan jihar nan

A ƙarshe ya roƙi ƙungiyoyin Adaidai Sahu na jihar Kano da su zama haɗa kansu domin ciyar da jihar Kano gaba

Shugaban Hukumar KAROTA Engr Faisal Mahmud Kabir
Ya karbi baƙuncin ƙungiyoyi daban daban wadanda suka zo domin ƙulla alaƙar aiki da Hukumar KAROTA.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

‘Yan Takarar Gwamnoni A Jam’iyyar PRP Sun Koma SDP

Published

on

‘Yan takarar gwamna a karkashin jam’iyyar PRP a zaben 2023 na sun sauya sheka zuwa jam’iyyar SDP.

Shugaban kungiyar ‘yan takarar gwamnan a PRP Malam Hayatuddeen Lawai Makarfi ya tabbatar da ficewarsu daga PRP zuwa SDP.

Shugaban kungiyar ya bayyana cewa sun dauki matakin koma SDP ne domin tsamo kasar nan daga halin da take ciki.

Lawai Makarfi wanda ya yi takarar gwamna a jam’iyyar ta PRP a Jihar Kaduna, ya bayyana cewa mutane na sauya sheka zuwa SDP ne bisa yadda da shugabancinta.

Makarfi ya ce sauya shekar su wani shiri ne na hadin domin kubtar da Najeriya daga shugabanci mara kyau, inda kuma ya nuna damauwarsa bisa yadda ake ci gaba da samun zubar jini, karuwar takauci, ya yin da hukumomin gwamnati ke durkushewa, inda kuma jam’iyyar APC da PDP suka mayar da mulkin kasar tamkar kasuwanci.

Kungiyar ‘yan takarar gwamnan ta kuma mika godiyarta ga PRP bisa damar da ta ba su a siyasa, inda suka ce a halin yanzu sun koma kan hanyar gaskiya.

Shugaban jam’iyyar SDP Malam Shehu Musa Gabam ya shaida musu cewa jam’iyyar za ta bai’wa masu sauya shekar dukkan wata dama da ta kamata.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Kaduna Za Ta Dauki Ma’aikatan Lafiya Sama 1,000

Published

on

Gwamnatin Kaduna Jihar ta amince da daukar ma’aikatan lafiya 1,800 a fadin Jihar.

Kwamishiniyar lafiya ta Jihar Hajiya Umma Ahmad ce ta tabbatar da hakan ta cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Alhamis.

Sanarwar ta ce gwamnatin Jihar karkashin jagorancin gwamna Malam Uba Sani za a dauki Ma’aikatan ne domin cike gurbin Ma’aikatan a dukkan cibiyoyi kiwon lafiya matakin farko na Jihar.

Sanarwar ta kara da cewa daukar Ma’aiktan hakan zai kara tabbatar da ci gaban Jihar akan matsayin da ta ke dashi a fannin kiwon lafiya matakin farko a Najeriya.

Kwamishinyar ta kuma ce daukar ma’aikatar zai kawo karshen karancin ma’aikata da ake samu a cibiyoyin kiwon lafiyar, tare da raguwar yawaitar mace-macen mata masu juna biyu da kananan yara, da kuma kara inganta lafiyar mutanen Jihar.

Acewarta a halin yanzu ana ci gaba da gyaran cibiyoyi 255 na kiwo lafiya matakin farko, yayin da za a daga martabarsu zuwa mataki na biyu, da samar da kayan aiki na zamani, tare da bayar da muhimman magunguna duk a kokarin da gwamnatin Jihar ke yi na inganta bangaren kiwon lafiya.

Kwamishinar ta kuma ce cibiyoyin za su dunga aikin duba masu cutuka daban-daban da suka hada da ciwon suga da bai yi karfi ba, hawan jini shima da bai yi karfi ba, da bayar da tallafin wajen haihuwa da dai sauransu.

Continue Reading

Labarai

Majalisar Wakilan Za Ta Haramtawa Masu Shekaru Sama Da 60 Tsayawa Takara

Published

on

Majalisar wakilan Najeriya ta tsallake karatu na biyu kan kudurin da zai haramtawa ‘yan takarar shugaban Kasa, da na gwamnan masu shekaru sama da 60 tsayawa takara.

A zaman Majalisar na yau Alhamis, da kudurin ya tsallake karatu na biyu, bayan da dan Majalisar Hon Ikeagwuonu Ugochinyere ya dauki nauyin kudurin da ke bukatar canza wasu bangarori na kudin tsarin mulkin Kasa na shekarar 1999.

Rahotanni sun bayyana cewa da zarar kudurin ya tsalle karatu na uku, kuma shugaban Kasa ya sanya hannu akansa, hakan zai sauya fasalin tsayawa takara a Kasar.

Daga cikin abubuwan da kudurin ya kunsa sun hada da, dukkan wanda ya haura shekaru 60 da haihuwa b azai tsaya takarar shugaban Kasa ba, ko gwamna a Kasar.

Sannan kuma wajibi dukkan dan takara ya kasance ya mallaki shedar digirinsa na farko a bangaren da ya fi kwarewa akai, a matsayin mafi karancin takardar karatu.

Ya yin da kuma kudin ya bukaci yin gyara a sashe na 131 na kudin tsarin mukin Kasa, na bukatar iyaknce shekaru ga kowanne dan takarar shugaban Kasa, tare da sashi na 177 ga gwamomin Jihohi.

Baya ga wannan kuduri majalisar ta kuma amince da wasu kudurori daban-daban da suka shafi ci gaban Najeriya.

 

Continue Reading

Trending

%d bloggers like this: