Connect with us

Labarai

Karota Za Su Cigaba Da Kama Masu Tuƙa Adaidaita Sahu Ƴan Ƙasa Da Shekara 18

Published

on

 

Hukumar kula da Zirga-zirga Ababen Hawa ta jiha KAROTA ta ce zata ci gaba kama yaran da shekarunsu bai kai 18 ba waɗanda suke tuƙa Baburin Adaidai Sahu.

A wata sanarwa da kakakin hukumar Nabulisi Abubakar K/Naisa ya sanyawa hannu, ya ce Shugaban Hukumar KAROTA Engr Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana haka, lokacin da yake karbar baƙuncin gamayyar ƙungiyoyin Adaidai Sahu na jihar nan, ƙarƙashin jagorancin Alh. Mansur Tanimu

Engr. Faisal ya ce Hukumar KAROTA ba za ta lamunci bawa ƙananan yara wandanda shekarunsu bai kai 18 ba tuka Adaidai Sahu

Haka kuma, Hukumar ba za ta yadda da yin amfani da waya a lokacin tuki ba, da kuma ɗaukar kayan da suka wuce kima a cikin Adaidai Sahu

A nasa jawabin Shugaban Gamayyar Ƙungiyar Adaidaita Sahu ta jihar Kano Alh. Mansur Tanimu ya ce sun zo Hukumar KAROTA ne domin taya murna ga sabon shugaba tare da alkawarin bayar da haɗin kai domin ciyar da jihar Kano ta ɓangaren sufuri gaba

Ya bayar da tabbacin bawa Hukumar KAROTA haɗin kai domin ciyar da jihar Kano gaba

A wani cigaban kuma, shugaban Hukumar ya karɓi baƙuncin kungiyar Adaidai Sahu ta Kwankwasiyya kar ƙarƙashin jagorancin Comr. Nazifi BK Gidan Kuɗi,

Sun roƙi Gwamnatin jihar Kano ta samar da makaranta wadda za ta dinga bayar da horo ga matuƙa Baburan Adaidai Sahu na faɗin jihar nan hakan zai taimaka wajen rage yawan aikata laifukan tuki titinan jihar nan

A ƙarshe ya roƙi ƙungiyoyin Adaidai Sahu na jihar Kano da su zama haɗa kansu domin ciyar da jihar Kano gaba

Shugaban Hukumar KAROTA Engr Faisal Mahmud Kabir
Ya karbi baƙuncin ƙungiyoyi daban daban wadanda suka zo domin ƙulla alaƙar aiki da Hukumar KAROTA.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mafarauta 18 A Taraba

Published

on

Ƴan bindiga sun kashe mafarauta 18 a wani harin da suka kai a ƙaramar hukumar Bali da ke jihar Taraba.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe mafarautan 15 ne a wata arangama da ƴan bindiga a wani dutse kusa da garin Maihula a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba.

An ruwaito cewa ƴan bindigan da yawansu ya haura 200 sun yi yunƙurin kai hari a garin Bali Shalkwatar ƙaramar hukumar Bali, da wasu ƙauyukan da ke kewaye amma mafarautan sun yi artabu da su.

Ƴan bindigan waɗanda suke ɗauke da miyagun bindigu da suka fi na mafarautan, sun halaka mafarauta 15 a yayin artabun.

Wata mazaunin yankin mai suna Musa Umar ya bayyana cewa, mafarauta 14 ne suka mutu a wurin artabun, yayin da wasu mafarauta da dama suka samu raunuka, ɗaya kuma ya mutu a hanyar zuwa Asibitin Jalingo wanda adadin ya kai 15.

Shugaban kungiyar mafarauta na jihar Taraba, Adamu Dantala ya bayyana cewa an kashe mambobinsa 15 a wata arangama da ƴan bindiga.

Ya ce ƴan bindigan sun kuma yi wa mambobinsa kwanton ɓauna a kusa da garin Dakka a ƙaramar hukumar Bali inda suka kashe mafarauta uku.

 

Continue Reading

Labarai

Gwamnatin Tinubu Za Ta Inganta Tsaro Da Bunƙasa Tattalin Arziƙi – Fadar Shugaban Ƙasa

Published

on

A kasafin kudin shekara mai zuwa ta 2024, Bola Ahmed Tinubu ya ce babban abin da zai dage a kai shi ne tsaro da zaman lafiya a ƙasa Najeriya.

Fadar shugaban kasa ta ce shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sha alwashin samar da ayyukan yi tare da farfado da tattalin arzikin Najeriya.

A jawabin da ya gabatar, Bola Tinubu ya ce za a yiwa tsarin tsaro kwaskwarima a Najeriya domin a tsare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kundin kasafin kudin shekarar 2024 ya fi karkata zuwa ga wasu abubuwa takwas, kamar yadda mai magana da yawun shugaban ƙasa Ajuri Ngelale ya sanar a jiya Laraba.

Daga cikinsu akwai samar da hanyar da masu hannun jari za su kawo kudi domin yin kasuwanci wanda hakan zai inganta tattalin arziki.

Gwamnatin Tinubu za ta kara tsayawa tsayin-daka wajen yakar talauci da zarar an amince da kasafin kudin na 2024 a majalisun tarayya.

Kasafin kudin 2024 ya bada karfi a abin da ya shafi cigaban al’umma, musamman kananan yara wanda sai da su ake cigaba.

 

Continue Reading

Labarai

Ƴan Bindiga Sun Hallaka Manoma Mutane Biyu A Taraba

Published

on

Wasu da ake kyautata zaton ƴan bindiga ne sun kashe manoma biyu a gonakinsu a yankin Yangtu a jihar Taraba.

Kamar yadda Channels tv ta ruwaito, lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a kudancin jihar da ke shiyyar Arewa maso Gabas.

Tsohon ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Ussa a majalisar dokokin Taraba, Habila Timothy, ya bayyana cewa manoman sun fito ne daga ƙauyen Kpambo.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa manoman sun je gonarsu da ke Kwambai, garin da ya haɗa iyaka da ƙaramar hukumar da kuma yankin Yangtu.

A nasa ɓangaren, jami’in hulɗa da jama’a na rundunar yan sandan jihar Taraba, Abdullahi Usman, ya ce har yanzu rahoton bai kai ga ofishin ƴan sanda ba.

Ya kuma ƙara ba da tabbacin cewa hukumar ta ɗauki matakai kuma an yi nisa a kokarin kakkabe yan bindiga gaba ɗaya daga jihar.

 

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: