Kwamitin amintattu a jam’iyyar NNPP a Najeriya sun sanar da dakatar da jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso daga cikinta.

Jam’iyyar ta naɗa Dakta Agbo Major a matsaayin shugaban jam’iyyar na riko da wasu mukamai 19.

An dakatar da Sanata Rabi’u Kwankwaso tsawon watanni shida daga jam’iyyar.

Kamfanin dillancin labarai naa ƙasa NAN ya ruwaito cewar dakatarwar ta biyo bayan wani taro da jam’iyyar ta gudanar a jihar Legas yau Talata.

Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar Babayo Muhammed Abdullahi ya bayyanawa manema labarai cewa sun dakatar da Kwankwaso bayan zargin cin dunduniyar jamiyyar wajen taimakawa shugaba Bola Tinubu.

Haka kuma sun dakatar da shi ne bisa dokar kundin tsarin gudanarwar jam’iyyar ya tanada.

Tun tuni jam’iyyar ta zargi Sanata Kwankwaso da cin dunduniyarta, wanda ta ce ya yi amfani da su ne wajen taimakawa siyasar Shugaba Bola Tinubu na Najeriya.Kwamitin amintattu a jam’iyyar NNPP a Najeriya sun sanar da dakatar da jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso daga cikinta.
Jam’iyyar ta naɗa Dakta Agbo Major a matsaayin shugaban jam’iyyar na riko da wasu mukamai 19.
An dakatar da Sanata Rabi’u Kwankwaso tsawon watanni shida daga jam’iyyar.
Kamfanin dillancin labarai naa ƙasa NAN ya ruwaito cewar dakatarwar ta biyo bayan wani taro da jam’iyyar ta gudanar a jihar Legas yau Talata.
Sakatare a kwamitin amintattu na jam’iyyar Babayo Muhammed Abdullahi ya bayyanawa manema labarai cewa sun dakatar da Kwankwaso bayan zargin cin dunduniyar jamiyyar wajen taimakawa shugaba Bola Tinubu.
Haka kuma sun dakatar da shi ne bisa dokar kundin tsarin gudanarwar jam’iyyar ya tanada.
Tun tuni jam’iyyar ta zargi Sanata Kwankwaso da cin dunduniyarta, wanda ta ce ya yi amfani da su ne wajen taimakawa siyasar Shugaba Bola Tinubu na Najeriya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: