Jami’an sojin Najeriya sun hallaka wasu ‘yan bindiga Hudu a wani sumame da suka kai maboyarsu da ke kauyuka daban-daban na Jihar Zamfara.

 

Mai magana da yawun rundunar Operation hadarin daji Kaftin Yahya Ibrahim ne ya bayyana hakan.

 

Ibrahim ya ce jami’an sun kai harin ne a kauyukan Tazame, Mashema, Maje, Doka, Gandaya, duk da ke karamar hukumar Bungudu ta Jihar.

 

Kaftin Yahya ya kara da cewa jami’an sun kuma sake kai hari maboyar batagarin, a wani daji da ke kewaye da kauyen Gandaya da ke karamar hukumar ta Bungudu.

 

Ibrahim ya bayyana cewa da yawa daga cikin ‘yan bindigar sun tsere dauke da raunuka a tare da su, sannan sun lalata sansanonin bata garin.

 

Kazalika ya ce jami’an sun kuma kwato shanu 57 kayan sojoji da kuma tsabar kudi naira 900,000 da sauran wasu kayayyaki.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: