Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ya bayyana kwarin gwiwarsa a game da hukuncin Kotun Koli.

Abba Kabir ya bayyana haka ne a jiya Lahadi 24 ga watan Disamba a filin wasa na Sani Abacha yayin bikin horas da matasa 2,500 a jihar.
Gwamnan ya yabawa alkalan kan yadda suka dage don ganin sun yi adalci kan shari’ar da ke gabansu.

Ya kuma yi kira ga jama’ar jihar da su kwantar da hankalinsu da kuma kara musu karfin gwiwa kan alkalan kotun.

Abba Kabir ya tabbatar wa magoya bayansa cewa ya na da tabbacin samun nasara a shari’ar da za a yanke.
Wannan na zuwa ne bayan da kotunan baya su ka soke nasararsa.
Gwamnan ya sake daukaka kara zuwa Kotun Koli inda a ranar Alhamis 21 ga watan Disamba ta zauna domin sauraron korafin