A yau ake gudanar da zaben shuwagabannin kananan hukumomi a jihohin Kaduna da Kogi.

A jihar Kaduna jam’iyyar 10 ne su ka shiga zaben.


Akwai masu neman kujerar shugabannin kananan hukumomi guda 79 wadanda su ka shiga zaben
Shugaban hukumar zabre mai zaman kanta a jihar Farfesa Joseph Gambo ne ya shaida haka.
Sai dai gwamna Uba Sani na Jam’iyyar APC ya ce jam’iyyar su ce za ta lashe dukkanin kujerun.
Batun da ya hifar da cecw kuce.
A jihar Kogi ma ana gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi da kansiloli a yau.
Gwamnatin jihar ta tabbatar da cewar za a gudanar da zaben cikin zaman lafiya da kwanciyar hankali.