Gwamnatin jihar Neja ta sanar da ƙudurinta na raba manyan motocin kayan abinci guda 1,000 akan farashi mai sauƙi a ɗaukacin ƙananan hukumomin jihar 25, a matsayin tallafi ga al’ummar jihar duba da gabatowar azumin watan Ramadan.

Gwamnan jihar Umar Bago ne ya sanar da wannan ci gaban, yayin ganawa da masu ruwa da tsaki a gidan gwamnatin Jihar da ke Minna.
Bago ya ƙara da cewa dalilin ganawar ta su na da alaƙa ne da yadda za a tsara saukar da farashin kayan abinci, ga al’ummar jihar a lokacin gudanar da ibadar azumin watan Ramadan.

Ya kuma bayyana cewa gwamnatin jihar bisa haɗin guiwa da wani ɓangare mai zaman kansa na Niger Foods, sun girbe miliyoyin ton-ton na kayan abinci, waɗanda za su wadatar da al’ummar jihar.

Yayin da kowacce ƙaramar hukuma za ta karɓi mota goma ta kayan abinci duk bayan kwana goma a cikin watan na Ramadan, wanda za a siyar da shi a bisa sauƙaƙƙen farashi.
Gwamna Bago ya ƙara da cewa za a dinga siyar da kayan abincin mai sauƙi da kaɗan-kaɗan, dan tabbatar da kowa ya samu damar mallaka, Daɗin daɗawa kuma, za a raba motoci 500 kyauta ga al’umma marasa ƙarfi a faɗin jihar.
Ya kuma gargaɗi masu alhakin siyar da kayan abincin da su yi aiki bisa nagarta, tare da cewa duk wanda aka kama da rashin gaskiya zai fuskanci hukunci.