Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai tare da nuna damuwar kan kisan gillar da aka yiwa wasu mafarauta a Jihar Edo.

Alhaji Atiku ya bayyana hakan ne ta cikin wata wallafa da ya fitar a yau Juma’a, yana mai bayyana cewa a yiwa dukkan wadanda aka kashe adalci.

Atiku ya bukaci hukumomin Kasar da su gagauta gudanar da cikakken bincike tare da yin komai a bayyana ne don daukar matakin doka akan wadanda suka yi aika-aikar.

Atiku ya kuma mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalai da ‘yan uwan wadanda aka kashe .

Leave a Reply

%d bloggers like this: