Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP a Najeriya sun lashi takobin karbe dukkan ikon kujerun shugabanci daga jamiyyun hamayya.

Shugaban kungiyar Bala Mohammed gwamna Bauchi shi ne ya bayyana haka yau a Enugu yayin jawabin buɗe taron ƙungiyar.

A cewarsa, tsarin da su ka yi ya sha bamban da da sauran tsarukan da su ke yi a baya.

Taron dai ya mai da hankali don tattauna ayyukan da su ka shafesu

A cewar Bala Muhammad tsarin da za su fito da su yi zai taimaka wajen karbe madafun iko daga jam’iyyun adawa

An gudanar da taron ne a gidan gwamnatin Enugu.

Gwamnonin jam’iyyar PDP na jihohin Delta, Edo, Filato, Taraba, Zamfara, Oyo da Akwa Ibom.

Sauran sun haɗa da Adamawa, Bayelsa, Eungu da Bauchi ne su ka halarta.

Leave a Reply

%d bloggers like this: