Gwamnatin Jihar Kano ta mayarwa da Jami’ar Yusuf Maitama Sule tsohon sunanta na asali.

Majalisar Zartarwar jihar ce ta dauki matakin mayarwa da Jami’ar tsohon sunanta, bayan wani taro da gwamna Abba Kabir Yusuf ya jagoranta a jiya Juma’a.

Idan ba a manta ba dai a watan Yulin shekarar 2017 ne tsohon gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya canjawa jami’ar suna zuwa Jami’ar Yusuf Maitama Sule, domin tunawa da marigayi Dan Masanin Kano Yusuf Maitama Sule, bisa irin gudummawar da ya bai’wa Jihar, dama Kasa baki daya.

 

Sai dai kuma a halin yanzu gwamnatin Jihar mai ci karkashin Jam’iyyar NNPP ta dauki matakin dawowa da Jami’ar tsohon sunanta.

Northwest University ya samo asali ne a zamanin mulkun tsohon gwamnan Jihar Dr Rabi’u Musa Kwankwaso ya samar da ita.

Leave a Reply

%d bloggers like this: