Rundunar sojin Najeriya ta ce jami’anta sun samu nasarar hallaka ‘yan ta’adda 135, tare da kama mutane 185 da ake zargi da aikata laifuka, da kuma ceto mutane 129 da aka yi garkuwa da su a sassa daban-daban na fadin Kasar nan a cikin mako guda.

Daraktan yada yada labaran hedkwatar tsaro ta Kasa Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana hakan ne a yau Asabar a hedkwatar da ke Abuja.

Buba ya ce daga cikin wadanda aka kama ciki harda 61 da ake zargi da satar mai.

Acewar Buba ‘yan ta’adda a yankin Arewa ta tsakiya sun fara mika wuya ga sojojin su.

Leave a Reply

%d bloggers like this: