Rundunar sojin saman Najeriya reshen jihar Kano ta samu nasarra kama wani rikakken mai garkuwa da mutane .

 

An kama Abdul Isah a garin Durbunde da ke ƙaramar hukumar Takai a Kano.

 

Mai magana da yawun rundunar ta ƙasa Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya tabbatar da haka wanda ya ce sun kamashi ne a yammacin jiya Litinin.

 

Ya kara da cewa sun kamashi ne bayan samun bayanan sirri a dangane da mabiyarsu shi da yaransa.

 

Wanda aka kama ana zarginsa da yin garkuwa da mutane a yankunan.

 

Daga cikin mutanen da ake zargin ya yi garkuwa da su har da wani Yakubu Ibrahim Tagaho wanda aka fi sani da Sarki n Noman Gaya.

 

Sun yi garkuwa da shi ne a ranar 6 ga watan Afrilu na shekarar da ta gabata a gidansa da ke Takai.

 

A halin yanzu wanda aka kama na tsare hannun jami’an sojin kuma ana ci gaba da bincike a kansa.

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: