Rundunar sojin Najeriya ta samu nasarar kama wasu masu garkuwa biyu, yayin da au ka dakile wasu hare-hare a jihohin Sokoto, Kaduna da Filato.

 

Hakan na ƙunshe a wata sanarwa da su ka wallafa a shafinsu na X wato Twitter.

 

Su ka ce sun samu nasara ne a jiya Laraba.

 

Sanarwar ta ce sun tarwatsa ƴan bindigan a kauyen Sarma da ke Tangaza a jihar Sokoto.

 

Bayan wuta da su ka buɗe musu sun kuma babur, harsashi, da bindiga kirar AK47 guda ɗaya.

 

A wani cigaban kuma jami’an sun daƙile wani hari a hanyar ƙauyen Kasu da ke Kafanchan a karamar hukumar Jema’a a Kaduna.

 

A wannna waje ma sun kwato babur guda, harsashi da sauran makamai sannan su ka kama mutane biyu da su ke zargi masu garkuwa ne.

 

A wani farmakin da su ka kai a jihar Filato, a ƙaramar hukumar Barikin Ladi sun kashe ɗan fashi guda a shingen bincike da ke Kaskara.

 

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: