A jihar Filato kungiyar kwadago ta rufe ofishin rarraba hasken wutar lantarki a Jos babban birnin jihar yayin da su ka gudanar da zanga-zangar lumana a yau.

 

 

 

Mambobin kungiyoyin sun cika a kofar shiga hukumar kula da lantarki ta ƙasa.

 

 

 

Yayin zanga-zangar an hango jami’an tsaron DSS, ƴan sanda, da hukumar kare faararen hula ta NSCDC.

 

 

 

Matakin rufe ofishin rarraba hasken lantakin ya biyo bayan ƙara farashin wutar da aka yi a kwanakin nan wanda ƙungiyar ta ce ba za ta lamunta ba.

 

 

 

Ƙungiyar ta buƙaci a soke batun ƙarin wutar wanda ta ce ba za ta lamunci haka ba.

 

 

 

Kungiyoyin sun ɗauki maatakin zanga-zangar ne wanda su ka karade ofisoshin rarraba wutar na jihohin Najeriya.

 

 

 

 

Leave a Reply

%d bloggers like this: