Rundunar ƴan sanda a jihar Zamfara ta tabbatar da mutuwar jami’inta da ke jagorantar ofishinsu na Wasagu.

 

Lamarin ya faru a safiyar jiya Laraba a Ɗanmarke da ke ƙaramar hukumar Bukkuyum a jihar

 

Sanarwar da yan sanda su ka fitar a yau Alhamis, ya ce jami’an soja a Operation Hadarin Daji ne su ka harbe baturen yan sandan mai suna SP Liman.

 

An harbe dan sandan a kai a shingen binciken sojin bayan kin gabatar da kansa.

 

Jagoran sojin a shingen binciken mai suna Hassan ne ya harbe dan sandan.

 

Jami’an ƴan sanda a Zamfara sun bukaci a gudanar da bincike tare da tabbatar da cewar an hukunta wanda ya aikata hakan.

 

Sannan sun bukaci shugabannin tsaron da su tabbata an dauki mataki a kai.

 

Sanarwar ta ce wajibi ne jami’an soji d ƴan sanda a samu fahimtar juna domin samar da tsaro da zaman lafiya.

Leave a Reply

%d bloggers like this: